Cikakken Jerin Jihohin Najeriya 24 Inda Ma'aikata Ba Su Bin Bashin Albashi

Cikakken Jerin Jihohin Najeriya 24 Inda Ma'aikata Ba Su Bin Bashin Albashi

BudgIT, wata kungiyar kare hakkin farar-hula, ta fitar da sakamakon wani bincike da ta yi a jihohin kasar inda ta nuna jihohin da ma'aikata ba su bin bashin albashi da kuma wadanda ma'aikatansu ke bin bashi na akalla wata daya ko fiye da hakan.

ABIN LURA: Za ku iya ceton rayuwar diya mace dake cikin hadari. Bada gudunmuwarka ga Patreon na Legit

A rahotonsa, BudgIT ta ce nuna cewa jihohi kamar Edo, Ebonyi, Ondo da Taraba da kawo yanzu ma'aikatansu na bin bashi na wata shida da fiye da hakan.

Taswira da ke nuna biyan albashi a Najeriya
Cikakken Jerin Jihohin Najeriya 24 Inda Ma'aikata Ba Su Bin Bashin Albashi. Hoto: @BudgITng.
Asali: Twitter

Ga Jerin jihohin da ma'aikata ba su bin gwamnati bashi zuwa karshen watan Yulin 2022.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

  1. Sokoto
  2. Borno
  3. Zamfara
  4. Katsina
  5. Jigawa
  6. Yobe
  7. Kano
  8. Bauchi
  9. Gombe
  10. FCT, Abuja
  11. Kebbi
  12. Niger
  13. Kaduna
  14. Kwara
  15. Enugu
  16. Oyo
  17. Ogun
  18. Ekiti
  19. Osun
  20. Lagos
  21. Akwa
  22. Ibom
  23. Rivers
  24. Bayelsa
  25. Anambra

Kara karanta wannan

WAEC 2022: Hazikan Dalibai 4 Da Suka Ci Jarrabawarsu Da Sakamakon A, Hotunansu Da Sakamakon

Wani sabon rahoto ya lissafa jihohi 12 da gwamnoninsu suka ki biyan albashin watanni a jihohinsu a lokacin da ya dace.

Rahoton da BudgIT ta fitar ya nuna cewa a jihohin, a kalla ma'aikata na bin bashin wata daya a ranar 28 ga watan Yulin 2022.

Kungiyar ta nuna rashin jin dadinta kan halin da ake barin ma'aikatan gwamnati a ciki.

BudgIT ta Fallasa Jihohi 12 Dake Rike da Albashin Ma'aikata Na Tsawon Watanni

A wani rahoton, BudgIT ta bayyana damuwarta kan yadda wasu gwamnatocin jihohi suka ki biyan albashin ma'aikata.

Jaridar The Cable ta ruwaito cewa, BudgIT ta sanar da hakan a wata takardar da ta fitar ranar Alhamis wacce Iyanu Fatoba yasa hannu, mataimakin shugaban yada labaran kungiyar da sadarwa.

Hukumar tace sakamakon bincikenta na albasbin 2022 na kasa ya nuna cewa a kalla jihohi 12 ne ke rike da albashin ma'aikata har zuwa 28 ga watan Yulin 2022.

Asali: Legit.ng

Online view pixel