Muna Bukatar Shirin Da Zai Daura Mu Sama Da Yan Ta’adda – Osinbajo Ya Fadawa Sojoji
- Yemi Osinbajo ya ce akwai bukatar gwamnatin Najeriya ta yi shirin da zai sanya su kan gaba da tunanin yan ta’adda
- Mataimakin shugaban kasa ya yi kira da sojoji da masu ruwa da tsaki da kara kaimi wajen kirkiran makamai a cikin gida
- Shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Farfesa Ibrahim Gambari yana cikin wadada suka halarci Taron Da Osinbajo ya jagoranta
Abuja - Mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo ya ce akwai bukatar gwamnatin Najeriya ta dauki matakin da zai sanya tunanin su gaba da ‘yan ta’adda da ke barna a fadin kasar. Rahoton Channels TV
Ya ce kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta a halin yanzu da barazanar da ke kunno kai, yana bukatar sojoji da sauran masu ruwa da tsaki su kasance cikin shiri tare da kara kaimi wajen kirkiran makamai a cikin gida.

Kara karanta wannan
Zai iya yin abin da ya ga da: FG ta fadi dalilin da yasa Buhari zai ba 'yan Nijar motocin N1.5bn
Wannan shi ne daya daga cikin muhimman abubuwan da Osinbajo ya mayar da martani akai a wani taron tattaunawa mai zurfi da ya halarta a Kwalejin Tsaro na kasa mai Taken "Tsarin Tsaro na Kasa a yammacin ranar Laraba.

Asali: Facebook
Osinbajo yace Idan aka yi la’akari da irin kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta, ya zama dole mu kasance da tsare-tsare da matakai da zai samu kan gaban da yanta’ada
Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!
An nakalto mataimakin shugaban kasar yana fadar haka a wata sanarwa da kakakinsa Laolu Akande ya fitar ranar Alhamis.
Sauran jami’an da suka halarci taron sun hada da shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Farfesa Ibrahim Gambari; Babban Hafsan Sojin Ruwa, Vice Admiral Awwal Gambo; Kwamandan Kwalejin Tsaro ta kasa Rear Adm. Murtala Bashir, da kuma wakilin Sufeto Janar na 'yan sanda da sauran manyan jami'an kwalejin

Kara karanta wannan
Dakile rashin tsaro a babban birnin tarayya: IGP ya umarci a zagaye Abuja da tulin jami'an tsaro
Bayan Umarinin Buhari, Sojoji Za Su Gudanar Da Wani Atisaye Mai Taken ‘Operation Babu
A wani labari kuma, Abuja - Hafsoshin jami’an tsaro sun fara aiwatar da umarnin shugaban kasa Muhammadu Buhari na dakatar da hare-hare da kashe-kashen da ‘yan ta’adda ke yi nan take. Rahoton LEADERSHIP
A jiya ne hafsoshin Rundunar sojoji suka kaddamar da wani Atisaye mai Taken “Operation Show No Mercy wato Nuna ‘Yan Ta’adda rashin Tausayi”.
Asali: Legit.ng