Dambazau Ya Bayyana Yadda Za a Shawo Kan Matsalar Garkuwa da Mutane Tsakanin Matasan Makiyaya Fulani

Dambazau Ya Bayyana Yadda Za a Shawo Kan Matsalar Garkuwa da Mutane Tsakanin Matasan Makiyaya Fulani

  • Laftanar Janar Abdulrahman Dambazau (mai ritaya) ya yi kira ga cewa a yi gagawan raba matasan Fulani da kwayoyi da makamai
  • Dambazau wanda tsohon minista ne na harkokin cikin gida kuma babban hafsan sojojin kasa ya yi wannan kiran ne a wani taro a Abuja
  • Tsohon ministan ya jaddada bukatar da ke akwai na daukan matakai domin magance garkuwa da mutane tsakanin matasa fulani a Najeriya

FCT, Abuja - Tsohon ministan harkokin cikin gida, Laftanar Janar Abdulrahman Dambazau (mai ritaya) ya bukaci a gaggauta karbe makamai da kwayoyi a hannun matasan Fulani a matsayin wani mataki na dakile garkuwa da mutane a kasar.

Dambazau ya yi wannan kiran ne a kasidar da ya gabatar mai taken "Matsalar Makiyaya Fulani" da ya gabatar a taron tsaro na makiyaya fulani a Abuja.

Kara karanta wannan

An kuma: Mummunan fashewa ta auku a Kano an rasa shaguna, mutum 20 sun jikkata

Dambazau Ya Bukaci a Raba Matasan Fulani Da Bindigu Da Kwayoyi
Dambazau ya bada shawarar yadda za a shawo matsalar garkuwa da mutane a tsakanin makiyaya fulani. Hoto: @HonDambazauMHR
Asali: Twitter

Jaridar Vanguard ta rahoto cewa an yi taron ne da nufin gano hanyoyi warware kallubalen da makiyaya fulani ke fuskanta a zamanin nan da nufin samar da tsaro a kasar.

An shirya taron ne da hadin gwiwa da kungiyar Miyetti Allah da Northern Consensus Movement, NCM.

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

A cewarsa, daya daga cikin matakan da za a dauka shine dakile samun makamai da kwace dukkan makaman da a yanzu ke hannun matasan fulani makiyaya.

Kalamansa:

"Ya kamata mu tsaftace kasar, ina nufin da taimakon NDLEA, ya kamata a yi yaki da shan miyagun kwayoyi a tsakanin matasan fulani.
"Ya kamata mu tabbatar da adalci da cigaban al'umma da ilimi da lafiyan makiyaya fulani tare da basu damar cigaba a cikin al'umma.
"Don cimma hakan, ya kamata a basu ingantaccen ilimi, lafiya da kuma koyar da su sana'o'i."

Kara karanta wannan

'An Kashe Kwamandan Boko Haram Da Mataimakinsa' Yayin Da Mafarautar Suka Yi Artabu Da 'Yan Ta'adda a Borno

Ya ce wata matsala kuma shine wasu makiyayan da ke zama a daji suna satar mutane don karbar kudin fansa.

Ya kara da cewa:

"A baya ana iya gane makiyayi da sandarsa da ya ke kiwon shanu, a yau da AK-47 da wasu makaman ake ganinsu kuma suna amfani da shi wurin kai wa mutanen kauyuka hari ko garkuwa da fasinjoji a manyan hanyoyi.
"An san makiyayi fulani da saukin kai, tausayi, gaskiya, da sadaukarwa amma a yau ana masa kallon dan fashin daji, makashi, mai fyade, barawon shanu da mai garkuwa."

'Yan Sanda Sun Kai Samame Maɓuyar Masu Garkuwa, Sun Ragargajesu Sun Ceto Mutane

A wani rahoton, 'Yan sanda a Abuja a safiyar ranar Laraba 1 ga watan Yunin 2022, sun ceto mutane hudu daga mabuyar masu garkuwa a Dutsen Dudu a unguwar Kuje sun kuma lalata maboyar yan ta'addan.

Rundunar yan sandan ta tabbatar da hakan cikin wata sanarwa da ta fitar kamar yadda jaridar Vanguard ta rahoto.

Kara karanta wannan

Da duminsa: Nakiya ta sake tashi a gidan giya yayinda yan PDP ke murnar nasarar Atiku

Asali: Legit.ng

Online view pixel