Cikakken Jerin Jihohin Najeriya Da Suka Fi Cin Bashi, Da Waɗanda Ke Kan Gaba Wurin Rashin Aikin Yi

Cikakken Jerin Jihohin Najeriya Da Suka Fi Cin Bashi, Da Waɗanda Ke Kan Gaba Wurin Rashin Aikin Yi

Halin da tattalin arzikin Najeriya ke ciki a yanzu yana shafar mazauna kasar da gwamnatocin jihohi a yankuna daban-daban hakan yasa suke karbo manyan bashi musamman tun shekarar 2020.

Kamar yadda aka sani, karancin samun kudaden shiga da ya shafi tattalin arzikin na da alaka da annobar COVID-19 wacce ta adabi kasashen duniya tun farkon 2019.

A cewar StatiSense, yankin kudu maso yammacin Najeriya ne kan gaba wurin karbar bashi a shekarar 2021 duba da cewa yankin ne ya karbi kashi 33 cikin 100 na bashin da jihohi 36 suka karba har da FCT a wannan shekarar.

Cikakken Jerin Jihohin Najeriya Da Ke Kan Gaba Wurin Cin Bashi, Da Wadanda Ke Fama Da Rashin Aikin Yi
Jerin Jihohin Da Suka Fi Yawan Bashi a Najeriya (Hotuna: @GovWike, Governor Babajide Sanwo-Olu, Governor Nasir El-Rufai, Governor Ben Ayade, @Hope_Uzodinma)
Asali: Facebook

A shekarar 2020, kudu maso kudu ne yankin da ke kan gaba wurin rashin aikin yi - inda ya ya ke kashi 25 cikin 100, kuma yankin ne ke kan gaba wurin jihohi masu yawan bashi don jihohin yankin suna cikin 10 na farko a jerin masu karbar bashin.

Kara karanta wannan

Yan bindiga sun kai hari Masallaci lokacin bude baki, sun kashe mutum 3, sun yi awon gaba da wasu

Ga jerin sunayen jihohin da suka fi yawan bashi a shekarar 2021 a kasa:

  1. Lagos
  2. Kaduna
  3. Rivers
  4. Ogun
  5. Cross River
  6. Imo
  7. Akwa Ibom
  8. Edo
  9. Bayelsa
  10. Delta

Ga kuma jerin jihohin da suka fi yawan mutane marasa aikin yi:

  1. Lagos
  2. Rivers
  3. A/Ibom
  4. Kaduna
  5. Imo
  6. Cross River
  7. Anambra
  8. Adamawa
  9. Delta, SS
  10. Abia

Wannan bayanan na cikin wani wallafa da hadimar Shugaban kasa, Lauretta Onochie ta yi na shafinta na Facebook.

Buhari: Na Ji Daɗin Yadda Masu Hannu Da Shuni Suka Gane Cewa Canja Najeriya Ba Aikin Mutum Ɗaya Bane

A wani labarin, Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ce ya yi farin cikin sanin cewa kusoshin Najeriya sun gane cewa canja kasar nan aikin kowa ne, The Cable ta ruwaito.

Kara karanta wannan

Yanzu-yanzu: Kotu ta yankewa Mubarak Bala hukuncin shekaru 24 a gidan yari

Kamar yadda kakakin shugaban kasa, Femi Adesina ya bayyana a wata takarda, Buhari ya yi wannan furucin ne a ranar Lahadi a wata liyafa ta girmama shugabannin kwamitin kasuwanci, siyasa, kafafen watsa labarai da sauran ma’aikata.

Dama a watan Janairun 2021 The Cable ta bayyana yadda Buhari ya zargi masu fada a jin kasar nan da kawo cikas ga gwamnatin sa.

Asali: Legit.ng

Online view pixel