Da duminsa:Tsohon shugaban majalisar dattawa ya kuduri aniyar gaje kujerar Buhari

Da duminsa:Tsohon shugaban majalisar dattawa ya kuduri aniyar gaje kujerar Buhari

  • Tsohon sanata, Abubakar Bukola Saraki ya bayyana kudurinsa na tsayawa takarar shugaban kasa a 2023
  • Saraki ya bayyana haka ne a yau Larana 26 ga watan Janairu, kamar yadda majiyoyi suka bayyana
  • A baya an samu wasu 'yan siyasan Najeriya daga jam'iyyu daban-daban da suka nuna sha'awarsu ta tsayawa takara

Wani rahoton The Nation ya bayyana cewa, tsohon shugaban majalisar dattawa Bukola Saraki ya nuna sha’awar tsayawa takarar shugaban kasa a 2023.

Ayyanawar tasa na zuwa ne bayan tsohon jagoran jam’iyyar APC Asiwaju Bola Ahmed Tinubu; Gwamnan Ebonyi, Dave Umahi, Dan Majalisar Dattawa, Orji Kalu, da tsohon Gwamnan Imo, Rochas Okorocha, suka bayyana tasu aniyar.

Tsohon sanata, Bukola Saraki na son ya gaji Buhari
Da dumi-dumi: Tsohon shugaban majalisar dattawa ya bayyana aniyarsa ta gaje kujerar Buhari | Hoto: thenationonlineng.net
Asali: Facebook

Saraki, tsohon Gwamnan Kwara ya ce yana da kyakkyawan tarihi na gudanarwa da gogewa wajen tafiyar da lamurra yadda ake bukata.

Kara karanta wannan

Ado Doguwa ya samu karuwar 'diya na 28, ya lashi takobin haifan 30 kafin 2023

An haifi Saraki a ranar 19 ga Disamba, 1962, dan Sanata ne a jamhuriya ta biyu, marigayi Olusola Saraki.

Ziyarar sa a Makurdi

Tun da farko dai dan siyasar ya ziyarci gwamnan jihar Benue, Samuel Ortom a ranar Talata a garin Makurdi, wanda ya kira mutumin kirki a jam'iyyar PDP, inji rahoton jaridar Punch.

Ya ce:

“Jam’iyyar siyasar da ba za ta iya tsara al’amuranta ba, ba ta cancanci ta jagoranci kasar nan ba. Jam’iyyar da ta shirya al’amuranta kuma a shirye take ta jagoranci kasar nan, ita ce PDP”.

A wani labarin, tsohon gwamnan jihar Imo, Sanata Rochas Okorocha, ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar shugaban ƙasa a zaɓen 2023.

Punch ta rahoto cewa Okorocha ya bayyana haka ne a wata wasika da shugaban majalisar dattawa, Sanata Ahmad Lawan, ya karanta a zaman yau Laraba.

Kara karanta wannan

Shugaba a 2023: Fulani sun yi watsi da 'yan takara daga Arewa, sun fadi zabinsu

A ranar Litinin, 31 ga watan Janairu, 2022, tsohon gwamnan zai yi jawabi a wurin taron manema labarai na duniya, inda ake sa ran zai yi ƙarin haske kan manufofinsa.

Asali: Legit.ng

Online view pixel