Watanni 3 Kafin Ya Bar Mulki, Kasashen Afrika Za Su Karrama Shugaba Buhari
- ECOWAS za ta karrama Muhammadu Buhari a dalilin kokarin da ya yi wa yammacin Afrika
- Kungiyar ta ce Shugaban Najeriya ya taka rawar gani wajen tabbatar da tsarin damukaradiyya
- Malam Garba Shehu ya fitar da jawabi, ya ce Shugaban ECOWAS ya yaba da kokarin mai gidansa
Qatar - Kungiyar ECOWAS ta kasashen yammacin Afrika ta ce za ta karrama Muhammadu Buhari saboda kokarin da ya yi a kan mulki.
Jaridar The Cable ta ce Garba Shehu ya bada sanarwar cewa ECOWAS za ta ba shugaban Najeriyan lambar yabo a dalilin cigaban da ya kawo.
Garba Shehu ya fitar da jawabi a ranar Talata yana cewa Shugaban kungiyar kasashen yankin, Umaro Sissoco Embalo ya shaida wannan.
Shugaban Bissau-Guinea, Umaro Sissoco Embalo ya yi wannan bayani ne a wajen wani zama da ya yi da Buhari a taron majalisar dinkin Duniya.

Kara karanta wannan
Sai Da Na Dage Da Addu'a Don Kawai Allah Ya Ba Tinubu Nasara, Gwamnan APC Ya Magantu
Taron majalisar dinkin Duniya
Rahoton ya ce shugabannin sun yi zaman ne a kan abin da ya shafi kasashen suke tasowa.
Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!
Da zarar an kammala taron a yau Laraba ake sa ran shugaban na Najeriya zai dawo gida bayan ya shafe ‘yan kwanaki a kasar Larabawan.

Asali: Twitter
Mai magana da yawun bakin shugaban Najeriyan ya ce kungiyar ECOWAS za ta sa sunan Mai girma Muhammadu Buhari a kundin tarihi.
Shugaba Embalo yake cewa takwaransa na Najeriya ya yi abin da ya fi na kowa a wajen goyon bayan tsarin farar hula a yammacin Afrika.
Embalo ya ce Buhari ya yaki wajen ganin bayan duk wani tsari da ba na farar hula don haka za a rika tunawa da shi a hedikwatar ECOWAS.
Yanzu haka kungiyar kasashen Nahiyar su na gina babban ofishin ECOWAS a babban birnin Abuja. Tribune ta fitar da wannan rahoto dazu.
A bangarensa, Buhari ya yi maraba da wannan karramawa, ya ce a Duniyar yau ta tsarin farar hula ne kurum za a iya kawowa al’umma cigaba.
Mata ba su da wakilci a Majalisa
Mutane 360 ake da su a zauren Majalisar wakilan Najeriya, amma kun samu labari cewa 13 kacal ne mata a cikinsu, kusan kashi 3.33% kenan.
A matan da suka lashe takarar 2023 akwai Zainab Gimba, Fatima Talba, Goodhead Boma, da tsohuwar Minista, Khadija Bukar Abba Ibrahim.
Asali: Legit.ng