'Yan Najeriya ne masu cin hanci da rashawa ba Buhari ba, Garba Shehu

'Yan Najeriya ne masu cin hanci da rashawa ba Buhari ba, Garba Shehu

- Mai magana da yawun shugaban kasa Garba Shehu bayyana cewa halayyar 'yan Najeriya ne matsalar Najeriya

- Matsayin Najeriya a cin hanci da rashawar duniya na nuna cin hanci da rashawan 'yan Najeriya ne

- Ya kuma bayyana cewa alkaluman da aka yi amfani dasu ba daidai bane a siffanta Najeriya da haka

Garba Shehu, mai magana da yawun shugaban kasa, ya ce faduwar Najeriya a kan tsarin cin hanci da rashawa na Transparency International ya nuna 'yan Najeriya, ba Shugaba Muhammadu Buhari ba, The Cable ta ruwaito.

A lissafin shekarar 2020 da aka fitar a ranar Alhamis, Najeriya ta sauka zuwa 149 daga cikin kasashe 180 da aka gudanar da binciken bayan sun sami maki 25 cikin 100.

Fadar shugaban kasa ta ki amincewa da matsayin, tana mai cewa bangaren TI a Najeriya ya kunshi mambobin kungiyar adawa.

Lai Mohammed, ministan yada labarai da al’adu, ya kuma ce rahoton ba gaskiya bane na idan akayi la'akari da kokarin da kasar ke yi na yaki da rashawa.

KU KARANTA: Wata 1 da aurensa, 'yan ta'addan Boko Haram sun kashe matashin jami'in Soja

'Yan Najeriya ne masu cin hanci da rashawa ba Buhari ba, Garba Shehu
'Yan Najeriya ne masu cin hanci da rashawa ba Buhari ba, Garba Shehu Hoto: News Wire NGR
Asali: UGC

Da yake magana a ranar Litinin lokacin da yake gabatarwa a gidan talabijin na Channels Television na Sunrise Daily, Shehu ya ce jerin bayanan yana nuna cin hanci da rashawa ne daga ‘yan Najeriya ba gwamnatin Buhari ba.

“Zan fada muku cewa wannan zancen TI ba hukunci bane a kan Buhari ko gwamnatinsa ko yakin da take yi da rashawa, zan fada muku cewa wannan hukunci ne a kan‘ yan Najeriya,

"Saboda idan kuka lura da abubuwan da suke amfani da su wajen fidda wannan matsaya, sun yi amfani da abubuwa guda takwas, shida daga ciki sun nuna Najeriya a matsayin sama ko kasa, Najeriya a matsayi daya,” in ji Shehu.

“Biyun da suka zauna a kansu, wadanda suka haifar da wannan koma baya, su ne ainihin matsalolin Najeriya. Suna magana ne game da al’adun siyasa na kasar nan, siyan kuri’u, ‘yan daba. Shin Buhari ne dan daba? Ba mu yin sata.

“Kuma lokacin da suke magana a kan bangaren shari’a, suna magana ne kan yadda ake ganin cin hanci da rashawa a bangaren shari’a. Wadannan hasashe ba da gaskiya bane.

"Haka ne, akwai batutuwa a wannan bangaren amma canje-canje da yawa suna faruwa a wannan bangaren ba zai yi kyau ba idan suka yarda da shi don haka ka karfafa wa wadannan jami’an shari’ar da suke a tsaye sannan kuma tsarin ya samu sauki.”

KU KARANTA: Gwamna Ganduje ya ƙaddamar da jami'an kula da dokar Korona 2,000

A wani labarin, Gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike, ya ce Gwamnatin Tarayya ba ta da gaskiya a yakin da take yi da rashin tsaro a kasar.

Wike, wanda yayi magana a cikin shirin Siyasar gidan talabijin na Channels TV ya ce gwamnati ta sanya siyasa a yakin ta na rashin tsaro.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel