Hadaddiyar Daular Larabawa ta hana jirage daukar 'yan Najeriya zuwa Dubai

Hadaddiyar Daular Larabawa ta hana jirage daukar 'yan Najeriya zuwa Dubai

- Hadaddiyar daular larabawa ta fidda sanarwar hana jirage daukar 'yan Najeriya zuwa Dubai

- Daular ta kara ka'idojin COVID-19 da hana jirage daukar wadanda ba daga Najeriya suka taso kai tsaye ba

- Sai dai hakan ya jawowa wasu wakilan tafiye-tafiye damuwa na samun saukin tafiyar fasinjoji

Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE) ta sanya sabbin tsare-tsaren tafiye-tafiye a kan matafiyan Najeriya sakamakon hau-hawar COVID-19 a karo na biyu.

Tare da sabbin ka'idoji wadanda a halin yanzu ba su damu da masu ruwa da tsaki ba musamman wakilan tafiye-tafiye, jiragen sama kai tsaye da suka fito daga Najeriya ne kawai yanzu ke da izinin tashi kai tsaye zuwa UAE.

Wannan yana nufin cewa ba a ba da izinin jigilar fasinja tare da 'yan Najeriya a cikin jirgin zuwa UAE ba.

KU KARANTA: An ceto wasu daga matasan takum 25 da aka sace

Hadaddiyar Daular Larabawa ta hana jirage daukar 'yan Najeriya zuwa Dubai
Hadaddiyar Daular Larabawa ta hana jirage daukar 'yan Najeriya zuwa Dubai Hoto: Emirates
Asali: UGC

Daily Trust ta ruwaito cewa wannan sabuwar ka'ida ta hana wasu kamfanonin jiragen sama daukar ‘yan Najeriya zuwa Dubai.

A cikin Sabunta Ka'idojin Balaguro da Filin Jirgin Sama na Dubai ya bayar, Gwamnatin Hadaddiyar Daular Larabawa ta ce:

“Dole ne fasinjoji su yi tafiya kai tsaye daga Najeriya zuwa Dubai. Babu wani fasinja da zai shigo Najeriya zuwa Dubai daga kowace kasa / tashar jirgi idan ya ziyarta ko kuma ya wuce ta Najeriya cikin kwanaki 14 da suka gabata. ”

Wannan ƙari ne ga sauran ka'idoji na COVID-19 kamar takaddun gwaji mai nuna kubutu daga cutar kuma ana buƙatar fasinjoji suyi saurin gwajin COVID-19, su sami sakamako mai nuna ba sa dauke da cutar cikin awanni huɗu na lokacin tashin su.

Wannan ci gaban na baya-bayan nan, kamar yadda aka sani, ya haifar da damuwa ga wakilan tafiye-tafiye da fasinjoji wadanda suka yiwa wasu kamfanonin jiragen sama hanya don samun ribar hanyar ta Dubai.

KU KARANTA: EFCC ta damke wasu daliban makarantar damfara a Abuja

A wani labarin, Tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Atiku Abubakar ya sake yin rigakafin Korona Pfizer-BioNTech COVID-19 Kashi na biyu, jaridar The Nation ta rahoto.

Mai taimaka masa a fannin yada labarai Paul Ibe ya tabbatar da hakan.

Tsohon mataimakin shigaban kasa da a halin yanzu yana Dubai, Hadaddiyar Daular Larabawa, ya yi allurar ta farko a ranar 6 ga Janairu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel