An ceto wasu daga matasan takum 25 da aka sace

An ceto wasu daga matasan takum 25 da aka sace

- Rundunar hadin kai ta 'yan sanda da sojoji sun samu nasarar kubutar da wasu matasan da aka sace

- An sace matasan ne a hanyarsu ta komawa gida daga daurin auren abokinsu a Wukari jihar Taraba

- Majiya ta tabbatar da kubutar 24 daga cikin 25 da aka sace a ranar Laraba da ta gabata

An ceto matasa Takum 24 daga cikin 25 da masu satar mutane suka sace a hanyar Wukari - Takum a jihar Taraba.

Daily Trust ta tattaro cewa rundunar hadin kai na sjoji da 'yan sanda daga Benue da Taraba sun samu nasarar kubutar da matasan ne a wani samame da suka kai a cikin dazuzzukan da ke jihohin Taraba da Benue awanni kadan da suka gabata.

Baba Muhammed dan uwan ​​wasu daga cikin matasan da aka kubutar ya shaida wa Daily Trust a wata hira ta wayar tarho cewa an ceto 24 daga cikin 25 da aka sace a ranar Laraba da ta gabata.

KU KARANTA: EFCC ta damke wasu daliban makarantar damfara a Abuja

An ceto wasu daga matasan takum 25 da aka sace
An ceto wasu daga matasan takum 25 da aka sace Hoto: The Guardian
Asali: UGC

Ya ce ana ci gaba da neman sauran mutum daya kuma an kai biyar daga cikin matasan da aka ceto asibiti a Takum don kula da su.

Muhammed, ya bayyana cewa anyi biki a Anguwan Rogo ward a garin Takum inda duk Matasan suka fito.

“Zan iya fada muku cewa matasa 24 daga 25 da aka sace an ceto su ne ta hanyar hadakar sojoji daga Jihohin Benue da Taraba.

"Mun gode wa Sojoji, 'yan sanda da duk wadanda suka taimaka wajen kubutar da matasa ciki har da' yan jarida don bayar da rahoton abin da ya faru" in ji shi.

An tattaro cewa an kama wasu daga cikin masu garkuwar kuma ba a biya kudin fansa don ceto ba.

"Wannan wani aiki mai kyau ne da sojoji suka gudanar wadanda suka fito daga jihohin Taraba da Benue" wani mazaunin Takum ya ce

A halin yanzu, 'yan sanda sun yi magana da kakakin rundunar 'yan sanda na Taraba DSP David Misal ya ce ba zai tabbatar da ceton Matasa a hukumance ba saboda yanzu an sauya masa wurin aiki.

"Na ji labarin kubutar da matasa 24 amma ba zan iya tabbatar muku a hukumance ba saboda a yanzu haka ina kan canjin wuri kuma mutumin da zai karbe ni bai riga ya sauka ba" DSP Misal ya ce.

KU KARANTA: COVID-19: Jihohi 7 a arewacin Najeriya za su mori tallafin $900,000

A wani labarin, Wasu ‘yan bindiga wadanda ake zargin masu satar mutane ne sun sace wasu matasa 25 a kan hanyar Wukari zuwa Takum da karfe 6 na yammacin Laraba.

Wata majiya mai tushe a Wukari da Takum ta shaida wa Daily Trust cewa matasan 25 na kan hanyarsu ta komawa Takum ne daga Wukari inda suka halarci bikin aure a lokacin da suka yi karo da shingen kan hanya da ’yan bindiga da ake zargin masu satar mutane suka yi.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel