Rahoto ya yi ikirarin cewa ana zawarcin Jonathan kan ya fito takara a APC
- Wani rahoto ya yi ikirarin cewa yan siyasa a APC na kokarin neman dan takarar Shugaban kasa da ya kamata gabannin zaben 2023
- Wata jaridar kasar ta ruwaito cewa ziyarar da gwamnonin APC suka kai wa tsohon Shugaban kasa, Goodluck Jonathan na siyasa ne
- Ziyarar da gwamnonin na APC suka kai masa ya kuma haifar da rade-radin shugabancin Jonathan a 2023
Wani rahoto da ya billo ya yi ikirarin cewa jam’iyyar All Progressives Congress (APC) na zawarcin tsohon Shugaban kasa, Goodluck Jonathan, domin ya fito takarar Shugaban kasa a inuwarta a 2023.
Rahoton wanda jaridar This Day ta kawo ya yi ikirarin cewa wasu shugabannin jam’iyyar na matsawa tspohon Shugaban kasar a kan ya duba yiwuwar amsa tayin.
Jaridar ta bayyana cewa wata majiya wacce ta nemi a boye sunanta ta ce gwamnonin APC wadanda suka ziyarci Jonathan don taya shi murnar cika shekaru 63, sun yi amfani da taron wajen yi masa tayin kujerar shugabancin kasar.

Asali: Twitter
Rahoton ya ci gaba da ikirarin cewa makusantan Buhari na goyon bayan yunkurin ganin Jonathan ya zama Shugaban kasa a 2023.
KU KARANTA KUMA: An sako daliban ABU 9 da aka yi garkuwa da su
A cewar ikirarin, makusantan Buhari sun yarda cewa Jonathan ba zai cutar da ra’ayin kungiyarsu ba saboda haka shine ya cancanci karban mulki idan aka mika ta kudu.
Wata majiya a sansanin Buhari wacce bata so a bayyana ta tace:
“Ya mika mulki cikin lumana sannan bai riki kowa ba saboda haka ba zai zama barazana ga ra’ayin arewa ba.”
Sai dai, a baya Jonathan ya sha karyata cewar yana da ra’ayin takarar Shugaban kasa. Tsohon Shugaban kasar ya bayyana arara cewa ya mayar da hankalinsa ne a kan gidauniyarsa.
A gefe guda, Ambasada Yahaya Kwande, jigon kungiyar dattawan arewa, ya nemi PDP ta mika tikitinta ga yankin arewacin kasar a 2023.
KU KARANTA KUMA: An kama wasu mutane biyu da suka yi wa dan sanda gashin tsire tare da cin namansa
Jaridar Nigerian Tribune ta ruwaito cewa tsohon jakadan na Najeriya a kasar Switzerland, ya yi bayanin cewa tsarin karba-karba baya cikin gudun tsarin mulkin kasar, cewa tsari ne na jam’iyyun siyasa don magance wasu matsalolin da Najeriya ke fuskanta.
Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng