Jihar Sokoto
Wasu mutum 20 sun nutse cikin ruwa a wani haɗarin jirgin ruwa da ya auki a jihar Sokoto. Mutanen sun nutse ne yayin da suka je samo makamashi a kan jirgin.
Rundunar sojin Najeriya ta hallaka akalla ‘Yan bindiga 14 a wani farmaki da suka kai tare da kwamushe shugaban ‘yan ta’addan a Arewa maso yammacin Najeriya.
Zababben gwamnan jihar Sokoto ya ce ya kafa kwamitin zai binciki yawaita kashe kudi da cin bashin da gwamnatinsa ke yi a tsawon shekarun da ya yi mulki a jihar.
Gwamnan jihar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal ya rantsar da sakatarorin din-din-din 23 da manyan daraktoci 15 a ranar 2 ga Mayu, yan kwanaki kafin mika mulki.
Mai martaba sarkin Musulmai, Alhaji Sa'ad Abubakar III, ya roki yan takarar da suka garzaya Kotu bayan shan kaye da su rungumi duk hukuncin da Kotu ta yanke.
Matashin dan majalisar da ya lashe zaɓen ɗan majalisa a Sokoto, Bashir Usman Gorau, ya ce daga noman da yake yi ne ya samu ya haɗa kuɗin kamfe domin zaɓe..
Wani matashi ne ya dankara ‘Dan majalisa da kasa bayan nasarorinsa a 2007, 2011, 2015 da 2019, hakan ya nuna Allah SWT ne yake bada mulki ga wanda ya so ga kowa
Hukumar zabe ta kasa mai zaman kanta (INEC) ta ayyana Gwamnan jihar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal a matsayin zababben sanata mai wakiltan yankin Sokoto ta kudu.
Rahoto ya bayyana cewa, dan takarar majalisar wakilai a Sokotoya lashe zabe a karo na biyu bayan da aka tsige shi a 2019, inda Kokani Bala Kebbe ya lashe zaben.
Jihar Sokoto
Samu kari