Manoma da Dama Sun Mutu Yayin da Yan Bindiga Suka Kai Hari Kauyuka 7 a Kebbi da Sokoto

Manoma da Dama Sun Mutu Yayin da Yan Bindiga Suka Kai Hari Kauyuka 7 a Kebbi da Sokoto

  • 'Yan bindiga sun yi ajalin rayukan manoma da yawa yayin sabon harin da suka kai ƙauyukan bodar jihohin Kebbi da Sakkwato
  • Rahotanni sun bayyana cewa 'yan ta'addan sun tarwatsa kauyuka 7, bisa tilas mutane suka gudu daga gidajensu
  • Gwamnatin jihar Kebbi ta tura kayan agaji ga waɗanda suka rasa mahallansu sanadin harin 'yan bindigan dajin

Kebbi, Sokoto - Mutane da yawa mafi yawanci manoma sun rasu yayin da wasu miyagun 'yan bindiga suka kai farmakin rashin imani kan ƙauyuka 7 a bodar jihohin Kebbi da Sokoto.

Jaridar Daily Trust ta tattaro cewa ƴan bindigan sun halaka mutane da dama kana suka kori wasu masu ɗumbin yawa daga gidajensu a garuruwan da ke arewacin Najeriya.

Harin 'yan bindiga a bodar jihohin Kebbi da Sakkwato.
Manoma da Dama Sun Mutu Yayin da Yan Bindiga Suka Kai Hari Kauyuka 7 a Kebbi da Sokoto Hoto: Dailytrust
Asali: UGC

Kauyukan sun hada da Zawaini Zawaini, Jangargari da Jaja a jihar Kebbi da kuma Karani da wasu uku duk a jihar Sakkwato da ke Arewa maso Yammaci.

Kara karanta wannan

Subhanallahi: Yan Bindiga Sun Sace Wani Babban Malamin Addini Da Wasu Mutum 6

Rahotanni sun bayyana cewa maharan sun tafka barna yayin harin ciki har da ƙona gidajen jama'a da banka wuta a shagunan 'yan kasuwar ƙauyukan.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Wane hali mazauna ƙauyukan suka shiga bayan harin?

An tattaro cewa mummunan harin da 'yan bindiga suka kai garuruwan ya tilasta wa mutane barin gidajensu kana suka nemi mafaka a matsayin 'yan gudun hijira a wasu ƙauyuka

Wasu bayanai sun nuna mutane da dama sun zama 'yan gudun hijira a ƙauyen Jarkuka da ke ƙaramar hukumar Arewa ta jihar Kebbi.

Wane mataki gwamnatin Kebbi ta ɗauka?

An ce Gwamna Nasiru Idris ya bayar da umarnin a raba kayan agaji ga wadanda suka rasa matsugunansu.

Wani jami'an gwamnatin jihar Kebbi ya shaida wa jaridar cewa gwamnan ya tura tawaga ciki har da kwamishinoninsa domin kai kayan tallafi ga waɗanda suka rasa gidajensu.

Kara karanta wannan

Da Dumi-Ɗumi: 'Yan Bindiga Sun Kai Kazamin Farmaki Fadar Mai Martaba Sarki, Sun Ƙone Mutum Ɗaya

Kwamishinan harkokin jin ƙai da tallafi, Muhammad Hamidu Jarkuka, da kwamishinan yaɗa labarai da al'adu na cikin tawagar kai agaji da gwamnan ya tura.

'Yan Bindiga Sun Kai Hari Fadar Basarake, Sun Kashe Mai Neman Shiga Jami'a

A wani rahoton kuma 'Yan bindiga sun kai farmaki fadar wani basarake, sun ƙona ɗalibi mai neman gurbin shiga jami'a a jihar Osun.

Jami'ar hulɗa da jama'a ta rundunar 'yan sanda reshen jihar Osun, Yemisi Opalola, ta tabbatar da aukuwar lamarin, ta ce tuni aka tura jami'an 'yan sanda zuwa yankin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262