Siyasar Najeriya
Kungiyoyin masu sa ido a kan zabe a Kano sun soki ayyana Abba Kabir Yusuf a matsayin zababben gwamnan Kano da INEC ta yi, suna cewa ba a gama tattara kuri'u ba.
Babbar jam'iyyara hamayya ta kasa watau PDP ta fara ɗaukar mataki kan mambobin da take zargi da cin amana yayin babban zaben 2023 da aka kammala kwanan nan.
Mai martaba Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero, da Sarkin Gaya, Aliyu Ibrahim Gaya sun mika sakon taya murna ga zababben gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf.
Wasu daruruwa mata sanye da bakaken kaya sun fito zanga-zanga a cikin garin Kaduna domin nuna fushinsu a abinda suka kira fashin nasarar zaben gwamna a jihar.
Ofishin Jamiyyar APC reshen jihar Zamfara ya Hadu da Harin Yan Jagaliya, Mutane Biyu Sun rigamu Gidan Gaskiya, Yayin da Akayi asarar Dukiya Mai yawa a Harin
Kwanaki kaɗan bayan kammaƙa zaben mambobinta, majalisar dokokin jihar Kogi ta dakatar da wasu 'yan majalisun jiha guda 9 da wasu shugabannin kananan hukumomi.
A wata takarda da ya aika wa shugaban majalisa, Mukhtar Bajeh, shugaban masu rinjaye a majalisar dokokin Kogi ya aje mukaminsa saboda karuwar nauyi a kansa.
Tsohon gwamnan jihar Ekiti, Ayodele Fayose ya ce yan siyasa da masu rike da madafun iko ne suka jefa Najeriya a matsaloki, ya ce babu abun da ya sauya tun 1979.
Tsohon mataimakin shugaban kasa a Najeriya, Atiku Abubakar ya bayyana sakonsa ga 'yan Najeriya a lokacin da aka fara Azumin watan Ramadana mai alfarma na bana.
Siyasar Najeriya
Samu kari