Siyasar Najeriya
Sanata Smart Adeyemi daga jihar Kogi, ya shawarci Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya ɗauki mataki kan gwamnan CBN, Godwin Emefiele da sauran masu hannu a canjin kudi.
Gwamnan jihar Gombe, Muhammad Inuwa Yahaya, ya rushe majalisar zartarwan jiharsa, ya ce duk wanda ya masa laifi ya yafe masa, sannan kuma ya roki su yafe masa.
Shugaban kasa, Muhammadu Buhari, ya ce kullum yana kirga ragowar ranakun da suka rage masa a ofis domin ya ƙosa ya mika ragamar mulki ga zababben shugaban ƙasa.
Gwamna Abdullahi Sule na jihar Nasarawa ya bayyana cewa ya samu labarin yadda wasu daga cikin mambobin majalisarsa suka yaƙe shi a lokacin babban zaben 2023.
Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Alhaji Atiku Abubakar, ya tabbatar da cewa ba zai juya da baya ba, lauyoyin da ya haɗa zasu tabbatar da zaben 2023 damfara ne.
Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umaru Zulum, ya sallami dukkan mambobin majalisar zartaswa ana saura kwana 4 gabanin sake rantsar da shi a zango na biyu.
Kotun koli a Najeriya ta kawo karshen gardama kan halascin takarar Asiwaju Bola Tinubu da Kashim Shettima, ta fatattaki karar da PDP ta shigar don soke tikitin.
Gwamnan jihar Borno Farfesa Babagana Umara Zulum ya bayyana cewa shi mutum ne saurin fushi, amma kuma baya yarda ya kwana da fushin wani mutum a cikin ransa.
Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa a halin yanzun ma'aikata sun fara janye jiki daga wurin Muhammadu Buhari suna komawa bangaren gwamnatin Bola Ahmed Tinubu.
Siyasar Najeriya
Samu kari