Manyan Labarai A Yau
Shugaban jam'iyyar APC na kasa (APC), Abdullahi Umar Ganduje, ya yi magana kan zaben gwamnan jihar Anambra. Ya nuna cewa lokaci ya yi da yakamata a samu canji.
Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayyana cewa ana samun nasarori sosai a yakin da ake yi da 'yan bindiga a jihar. Gwamnan ya ce hare-hare sun ragu.
Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya nada sabon sakataren gwamnatin jihar Kano. Gwamna Abba ya maye gurbin Baffa Bichi wanda ya kora daga kujerar.
Mai taimakawa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu kan harkokin mazabu ta ɓukaci 'yan Najeriya da su daina sukar gwamnati kan cire tallafin man fetur.
Jami'an rundunar 'yan sandan jihar Katsina sun samu nasarori kan 'yan bindiga. 'Yan sandan sun hallaka 'yan bindiga 11 tare da kwato dabbobi masu yawa da suka sace.
Hukumar raya Jos ta rusa kasuwar ƴankeke da ke kusa da asibitin koyarwa na jami'ar Jos, ƴan kasuwa sun koka saboda asarar da suka tafka da miliyoyin Naira.
Dan majalisa mai wakiltar mazabar Kaduna ta Arewa, Bello El-Rufai, ya tabo batun binciken da ake yi kan mahaifinsa kuma tsohon gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufai.
'Yan bindigan da suka tafka aika-aikar kashe dan majalisar dokokin jihar Anambra, sun fitar da bayani kan ta'addancin da suka yi. Sun ce sun harbe shi sau biyu.
Dakarun sojojin Najeriya sun samu gagarumar nasara kan 'yan ta'adda a jihar Zamfara. Sojojin sun hallaka 'yan ta'adda masu yawa tare da jikkata wasu da dama.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari