Matawalle
Ƴan sanda sun tabbatar da sun mayar da dukkanin motocin tsohon gwamnan jihar Zamfara, Bello Matawalle, da suka kwace gidajensa. Kotu ce ta umarci yin hakan.
Tsohon gwamnan jihar Zamfara ya bayyana dalilin ganawarsa da Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu da kuma yadda ya gana da Dangote, attajirin nahiyarmu ta Afrika.
Shugaban Najeriya, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, ya karɓi bakuncin tsohon gwamnan Zamfara, Bello Matawalle, da shugaban kamfanin Ɗangote Group, Aliko Dangote.
Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Gusau jihar Zamfara, ta umarci jami'an tsaron jihar, da su fito da motocin da suka kwashe a gidan Bello Matawalle.
Tsohon gwamnan jihar Zamfara Bello Matawalle, ya mayar da martani kan abinda ya kira da bita da kullin siyasa da ya ce sabon gwamna, Dauda lawal na yi masa.
Tsohon gwamnan jihar Zamfara, Bello Matawalle, ya bayyana cewa tun kafin ya zama gwamnan jihar Zamfara ya siyo da yawa daga cikin motocinsa da aka kwace masa.
Tsohon gwamna Matawalle ya ce an masa sata a gida, don haka 'yan sanda suka nemi ya kawo hujjar da ke tabbatar da an masa sata kuma da gaske an masa satar.
Tsohon gwamnan jihar Zamfara, Bello Matawalle, ya yi zargin cewa gwamnatin jihar Zamfara ta tafka masa sata a gidajensa wajen ƙwato motocin da tace ya sace.
Gwamnatin jihar Zamfara ta kawo karshen kace-nace kan yawan adadin motocin da 'yan sanda suka kwamuso daga gidan tsohon gwamna Matawalle, ta ce guda 40 ne.
Matawalle
Samu kari