Matawalle
Kwamred Abdullahi Kaura, hadimin tsohon gwamnan Zamfara, Bello Matawalle ya kirayi Gwamna Dauda Lawal Dare da ya yi murabus a kan mulki saboda rashin tsaro.
Hukumar DWI da ke rajin raya dimukradiyya ta bukaci Shugaba Bola Ahmed Tinubu da ya kafa dokar ta baci a jihar Zamfara don dakile 'yan bindiga da rashin tsaro.
Tsohon gwamnan jihar Zamfara, Bello Matawalle ya zargi Gwamna Dauda Lawal kan rashin tabuka komai a kan harkar tsaro, ya ce ba ya neman shawarar magabatansa.
Kakakin tsohon gwamnan jihar Zamfara, Anas Abdullahi Kaura ya yaba wa Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu bisa naɗa Bello Matawalle a matsayin muƙamin minista.
A lokacin da aka aka cire sunan Maryam Shetty, tsohon Gwamna Bello Matawalle zai iya rike kujerar Minista a gwamnatin Bola Ahmed Tinubu, hakan ya jawo suka.
Wasu 'yan Arewa sun soki Bola Tinubu da cewa bai zabo masu wakilai na kwarai ba, an ce daga Kudu an dauko kwararru da su ka san aiki, an taro tarkace a Arewa.
Masu garkuwa da mutane a jihar Zamfara sun yi barazanar auren 'yan mata hudu da ke hannunsu idan har iyayensu ba su biya kudin fansa N12m nan da mako daya ba.
Bello Matawalle, tsohon gwamnan Zamfara ya kara kokarin kwace mulki daga hannu gwamna Dauda Lawal a gaban kotun zaɓe, ya gabatar da shaidu 19 ranar Jumu'a.
Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal Dare ya bayyana cewa ya gaji gwamnati ba tare da samun ko sisin kwabo ba a lalitar gwamnatin jihar, bayan tulin bashi a jihar
Matawalle
Samu kari