Labarin Sojojin Najeriya
Babban Hafsan Hafsoshin Sojojin Najeriya (CDS), Janar Christopher Gwabin Musa, ya sha alwashin gano bakin zaren harin bam da sojojin Najeriya suka kai.
Malaman Musulunci daga Arewacin Nejeria sun yi ganawar sirri da Babban Hafsan tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa, kan harin da jirgin soja ya kai a Kaduna.
Gwamna AbdulRazaq na jihar Kwara ya ziyarci jihar Kaduna don yin ta'aziyyar mutanen da suka mutu a harin bam tare da ba da tallafin Naira miliyan 200.
A'ummar garin Tudun Biri, da sojoji suka yi sakarwa bama-bamai da ya kashe akalla mutum 100 sun musanya shigar da gwamnatin Tinubu kara kotu da neman diyyar N33bn.
Rundunar sojin kasan Najeriya ta ce ta samu nasarar fatattakar wasu 'yan bindiga daga dajin karamar hukumar Igabi, jihar Kaduna, ta kwato makamai da babura.
Naira biliyan 33 al'ummar Tudun Biri su ke nema daga aljihun gwamnati a matsayin diyyar rayuka saboda ana tsakiyar taron maulidi sojoji sun harbawa jama'a bam.
Sojoji sun kai hare-hare akalla takwas kan fararen hula a Najeriya a cikin shekaru shida, inda abin ya fi shafar Arewacin kasar kawai. Mutane da dama sun mutu.
Wasu miyagun yan bindiga sun yi wa ayarin wasu motoci kwanton bauna a jihar Rivers. A yayin harin yan bindigan sun halaka sojoji hudu da direbobi biyu.
Gwamnatin tarayya ta neman likitoci da daliban kiwon lafiya da su shiga aikin soja don bunkasa lafiyar jami'an sojin kasar. Tinubu na shirin gina kwaleji.
Labarin Sojojin Najeriya
Samu kari