Labaran garkuwa da mutane
An dauke daliban makaranta a jihohin Katsina, Zamfara, Nasarawa da Neja. ‘Dan Majalisan Sokoto ya ce satar ‘Yan makaranta zai iya nakasa sha’anin ilmi a Arewa.
Dakarun sojin Najeriya sun ceto ɗalibai huɗu da aka sace daga jami'ar jihar Nasarawa bayan matsin lambar da suka yi wa yan bindigam da ke tsare da su.
Kwana uku bayan harin da aka kai gidajen kwanan ɗalibai na wajen makaranta, yan bindiga sun nemi N80m a matsayin kuɗin fansar ɗaiban jami'ar jihar Nasarawa.
Mai magana da yawun bakin ‘yan sandan Najeriya, ACP Muyiwa Adejobi, ya bayyana cewa an kama wanda ya sace daliban FGC Yauri da wasu miyagun masu satar mutane.
Yayin da ake jimamin abinda ya faru a Gusau da Dutsin-Ma, yan bindiga sun ƙara sace ɗaibai 4 daga jami'ar jihar Nasarawa da ke Keffi ranar Litinin da daddare.
Rundunar 'yan sandan jihar Katsina ta bayyana cewa dakarunta sun yi nasarar kuɓutar da mutane 171 da aka yi garkuwa da su a faɗin jihar cikin watanni huɗu.
Babbar kotun tarayya da ke Abuja ta yankewa wasu mutum biyu da suka yi garkuwa da babban lauyan Najeriya, Mike Ozekhome, hukuncin daurin shekaru 20 a gidan yari.
Wata mahaifiya ta yi ta maza inda ta cafke wani ɗan ta'adda da ya save ɗiyarta sannan ya halaka ta bayan an ba shi kuɗin fansa masu yawa a Zariya.
Wasu tsagerun 'yan bindiga sun yi awon gaba da Manjo Janar mai ritaya, Duru bayan sun masa kwantan ɓauna a jihar Imo da ke Kudu maso gabashin Najeriya.
Labaran garkuwa da mutane
Samu kari