
Labaran garkuwa da mutane







A cikin tsakar dare 'yan bindiga sun yi garkuwa da tsohon mataimakin gwamnan jihar Nasarawa, Farfesa Onje Gye-Wado. Karin bayani na tafe a cikin wannan rahoto.

Tsagerun 'yan bindiga sun kutsa da karfin tsiya cikin fadar wani babban Basarake da ake ganin girmansa a jihar Filato, sun yi awon gaba da shi zuwa wani wurin.

Wani basarake mai daraja ta uku, Kwe Ando Madugu, wanda ke Karamar Hukumar Ussa ta Jihar Taraba ya sha da kyar a hannun wasu matasa da suka yi masa dukan tsiya.

Rundunrar 'yan sandan jihar Neja ta bayyana kame wasu mutum da ake zargin sun hallaka wani hakimi tare da sace 'yarsa da karbar kudin fansa a jihar da ke Arewa.

Tsagerun yan bindiga sun sace mata da dan hakimin kauyen Nasarawa a karamar hukumar Tsanyawa ta jihar Kano inda suka tafi da su zuwa wani wuri da ba a sani ba.

Kwamishinan yan sandan Kano, CP Mamman Dauda, ya tabbatar da sace mataɗdagacin garin Nasarawa a karamar hukumar Tsanyawa da ke jihar ranar 2 ga watan Afrilu.

Miyagun yan bindiga da Kotu ta ayyanasu a matsayin 'yan ta'adda sun sace ɗaliban makarantat sakandiren jeka ka dawo a yankin karamar hukumar Kachia, Kaduna.

Wasu tsagerin yan bindiga kai hari, sun halaka mutane bakwai sannan suka yi garkuwa da wasu 26 a garuruwa bakwai da ke karamar hukumar Mashegu ta jihar Neja.

Wasu tsagerun 'yan bindiga sun sace daliban jami'a guda biyu a jihar Zamfara, inda suka kutsagidan kwanan dalibai don aikata wannan mummunan barna da suka yi.
Labaran garkuwa da mutane
Samu kari