Yaki da ta'addanci a Najeriya
An samu matsala a Sakkwato bayan yan ta'addan Lakurawa sun gano lagon daukar wasu daga cikin matasan jihar a matsayin sababbin yan ta'adda domin karfafa ayyukansu.
Kungiyar Amnesty Int'l da ke rajin kare hakkin bil'adama a duniya ta zargi gwamnatin Sakkwato da jikkata wata matashiya, Hamdiyya Sidi saboda wani bidiyo.
Gwamnan jihar Kebbi, Dokta Nasir Idris ya mika sakon ta'aziyya ga al'ummar garin Mera da Sarkin Argungu biyo bayan harin da ƴan Lukurawa suka kai.
Mataimakin gwamnan jihar Kebbi, Abubakar Umar Tafida da mai martaba Sarkin Argungu sun halarci jana'izar mutum 15 da aka kashe a kauyen Mera kwanan nan.
Hedkwatar tsaron Najeriya ta bayyana wasu mutum tara da take nema ruwa a jallo a Arewa maso Gabas kan zargin ta'addanci da rikau, ta lissafo sunayensu.
Hedkwatar tsaro ta ƙasa watau DHQ ta bayyana cewa dakarun sojoji sun yi nasarar kashe ƴan ta'adda 481, sun kubutar da mutane 492 da aka yi garkuwa da su.
Wasu mahara da ake kyautata zaton ƴan bindiga nw sun hallaka matasa uku a yankin ƙaramar hukumar Barkin Ladi jiya Laraba, sun kuma lalata gonakin mutane.
Dakarun tsaron sa kai na jihar da aka fi sani da Askarawa sun yi artabu da yan ta’adda da su ka yi kokarin kai hari karamar hukumar Tsafe a jihar Zamfara.
Rundunar ƴan sanda reshen jihar Imo ta tabbatar da fashewar bom a kasuwar Orlu ta ƙasa da ƙasa da ke jihar Imo, ta ce miyagu 2 da suka dasa shi sun mutu.
Yaki da ta'addanci a Najeriya
Samu kari