Gwamnatin tarayyar Najeriya
Amurka ta bayyana cewa majalisar dattawan ƙasar da ta amince da naɗin kakadun ƙasar a wasu kasashen duniya ba har kawo yanzu cikinsu harda Najeriya.
Malam Uba Sani ya ziyarci shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu domin ƙara jan hankalin gwamnatin tarayya ta taimaka wa jiharsa a fannin noma, lafiya da tsaro.
Ma'aikatan majalisa sun lashi takobin garƙame majalisar tarayya NASS da sauran majalisun dokokin jihohi daga ranar Laraba har sai an cika musu buƙatarsu.
Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya shiga taron majalisar zartarwa karo na uku tun bayan hawan gwamnatinsa a fadar shugaban ƙasa da ke birnin tarayya Abuja.
Gwamnatin tarayya ta koka kan yadda abubuwa suka taru suka mata yawa ita kaɗai babu mai kama mata, ta ce abu ya kai inda ya kai domin da ƙyar take biyan albashi.
A yau aka wayi gari da rasuwar jakadan Najeriya a ƙasar Morocco kuma Magajin Garin Zazzau, Alhaji Mansur Nuhu Bamalli, wanda Allah ya yi wa rasuwa a jihar Legas.
Tsohon darakta janar na ofishin kasafin kuɗin tarayya, Bode Agusto, masanin tattalin arziƙi ya mutu yana da shekaru 68 a duniya ranar Alhamis, 19 ga wata.
Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya amince da naɗin sabon shugaban bankin masana'antu na ƙasa BOI, Dr Olasupo Olusi, bayan tsohon ya yi murabus da kansa.
Yanzu haka an fara aikin tantance Mista Ola Olukoyede a matsayin sabon shugaban hukumar yaƙi da masu cin hanci da rashawa EFCC a majalisar dattawa.
Gwamnatin tarayyar Najeriya
Samu kari