Jerin Sunaye: Najeriya, Masar da Sauran Kasashen da Amurta Ba Ta da Ambasada da Dalilai

Jerin Sunaye: Najeriya, Masar da Sauran Kasashen da Amurta Ba Ta da Ambasada da Dalilai

  • Amurka ta koka kan rashin jakadu a kasashen duniya akalla 31 ciki har da Najeriya da kuma Masar watau Egypt
  • Mathew Miller, mai magana da yawun gwamnatin Amurka, shi ne ya bayyana haka, inda ya ce har yau majalisa ba ta amince da naɗin Jakadun ba
  • Wannan bayani na Miller na zuwa ne yayin da Amurka ke tallafa wa Isra'ila, wadda ke ci gaba da ruwan bama-bamai kan Gaza tun bayan harin Hamas

White House, US - Amurka ta bayyana cewa har kawo yanzu ba ta da jakada a Najeriya duk da yadda dangantaka ke ƙara kyau tsakanin ƙasashen biyu.

A wani jawabi da kakakin gidan gwamnatin Amurka, Mathew Miller, ya wallafa a manhajar X, ya yi ƙarin haske kan ƙasashen da US ba ta da wakilai.

Kara karanta wannan

Da Dumi-Dumi: Peter Obi Ya Magantu Bayan Kotun Koli Ta Tanadi Hukunci Kan Karar da Ya Daukaka

Shugaban Amurka, Joe Biden, da shugaba Tinubu.
Jerin Sunaye: Najeriya, Masar da Sauran Kasashen da Amurta Ba Ta da Ambasada da Dalilai Hoto: Joe Biden
Asali: Twitter

A cewar Miller, har yanzu Amurka ba ta da jakada a Najeriya da wasu ƙasashe 31 saboda majalisar dattawan ƙasar ba ta kai ga amince wa da waɗanda aka naɗa ba.

Sunayen ƙasashe 31 da babu jakadan Amurka

Baya ga Najeriya, mun tattaro muku sauran ƙasashen da Amurka ba ta da wakilci a faɗin duniya, ga su kamar haka:

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

1. Lebanon

2. Isra'ila

3. Masar

4. Azerbaijan

5. Lithuania

6. Haiti

7. Tarayyar Afirka

8. Turkmenistan

9. Albania

10. Zimbabwe

11. Barbados

12. Peru

13. Ecuador

14. Cabo Verde

15. Laos

16. Nijar

17. Djibouti

18. Malaysia

19. Gabon

20. Burundi

21. Croatia

22. Guatemala

23. Liberia

24. Somalia

25. Bahamas

26. Colombia

27. Cambodia

28. Montenegro

Kara karanta wannan

Shugaba Tinubu Ya Fadi Abu 1 da Zai Faru da Jihohin Kasar Nan da Ba a Cire Tallafin Man Fetur Ba

29. Timor-Leste

30. Marshall Islands

31. Burkina Faso

Dangantakar Amurka da Isra'ila

Wannan na zuwa ne yayin da ƙasar Amurka ta nuna goyon bayanta ga Isra'ila kan ruwan bama-baman da take yi a gaza tun bayan harin da ƙungiyar Hamas ta kai kan 'yan ƙasar Isra'ila.

Joshua Iginla, shugaba kuma wanda ya kafa majami'ar Champions Royal Assembly ya roƙi shugabannin duniya su tabbata wannan yaƙin na Isra'ila da Gaza bai rikiɗe ya zama yaƙin duniya na III ba.

A wani bidiyo da ya wallafa a Youtube, Malamin addinin ya bayyana cewa ya hango babban yaƙi na tafe.

Antonio Guterres Ya Soki Isra'ila

A wani rahoton kuma Yayin da ake ci gaba da gwabza yaki tsakanin Isra'ila da Hamas, Majalisar Dinkin Duniya ta yi martani.

Sakataren Majalisar, Antonio Guterres ya zargi Isra'ila da saba dokokin kasa da kasa na jin kai a harin da su ke kai wa.

Asali: Legit.ng

Online view pixel