Arewa
Kakakin ƙungiyar dattawan arewa, Hakeem Baba Ahmed, yace zai goyo bayan Peter Obi da ƙanins Datti Baba Ahmed ne kadai idan su ne suka dace dace da yan Najeriya.
Bala Muhammed, gwamnan jihar Bauchi dake arewa maso gabashin Najeriya ya nada mace ta farko da ta zama Farfesa a Bauchi LG a matsayin sabuwar VC a jami'ar jiha
Kungiyar wasu matasa a tsakiyar arewacin Nigeria ta goyi bayan babban bankin kasa CBN, kan tsarin da ya fito da shi na cire kudade. tace tsarin zai taimaka
Sanata Sani Musa mai wakiltar mazabar Niger East ya ce ba shi da wata niyya na fita daga jam'iyya mai mulki a jihar zuwa PDP, ya ce makiya suka kirkiri rahoton.
Mai baiwa gwamnan Benuwai shawara kan harkokin tsaro ya bayyana cewa kwamishinan gidaje da raya karkara, Mista Ekpe Ogbu, ya kubuta daga hannun masu garkuwa.
Yan sanda sun kama wani Michael Joseph, dan damfarar ATM a jihar Bauchi dauke da katin ATM daban-daban guda 31 yayin da ya yi kokarin damfara wata baiwar Allah.
Gwamnan jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, ya mika sakon ta'aziyya bayan samun labarin rasuwar, Oba Salawudeen Fagbemi Obembe II, mai shekara 110 a duniya.
Daga cikin jihohin Najeriya 36, shida ne kawai suka taba samar da kakakin majalisun jiha mata tun bayan samun yanci a 1999, kudu na da 5 yayin da arewa ke da 1.
Dan takarar kujerar sanata a jam’iyyar PDP kuma mijin jarumar fim din kudu, Ned Nwoko, ya zargi mazan kudancin Najeriya da jefa mata da dama a harkar karuwanci.
Arewa
Samu kari