Abuja
Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta ba da umarnin cafke tsohon hafsan sojojin ruwa a Najeriya, Vice Admiral Usman Jibrin kan badakalar N1.5bn da wasu mutane biyu.
Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa mutane 1m ne kadai zasu ci gajiyar tallafin N50,000 da aka fara rabawa wanda za a ci gaba a karshen wannan wata da muke ciki.
Ministan Abuja ya nemi hadaka da kasar Hungary domin inganta noma da tsaro a birnin tarayya. Ya yi jawabin ne yayin wata ziyara da ya kai ofishin jakadancin kasar.
Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce ba za su ci gaba da zargin gwamnatin tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari ba kan halin da ake ciki.
ACP Olumuyiwa Adejobi, a wata zantawa da manema labarai a jihar Kaduna, ya ce an kama Ibrahim Mandi, wanda ake zargin ya kitsa harin jirgin kasan Abuja-Kaduna.
Kungiyar malaman jami’o’i reshen jami’ar Abuja ta tsunduma yajin aikin sai baba-ta-gani a ranar Ahamis, 2 ga watan Mayu, 2024 kan abubuwan da ke faruwa da kungiyar.
Kungiyar yan kasuwa TUC ta yi karin haske kan karin kaso ashirin da biyar cikin dari da kaso talatin da biyar da gwamnatin tarayya ta ce ta yi wa ma'aikata.
Attajirin Nahiyar Afirka, Aliko Dangote ya koka kan illar da faduwar darajar Naira ya yi ga kamfanoninsu inda ya ce suna kokarin shawo kan matsalar ba da jimawa ba.
Binciken kwa-kwaf ya gano gaskiya kan rade-radin da ake yaɗawa cewa Shugaban Bola Tinubu ya soke wasu hukumomin ICPC da NDDC da NCC da FRCN a Najeriya.
Abuja
Samu kari