Yan ta'adda
Jiragen yakin rundunar sojojin saman Najeriya sun samu nasarar halaka wani ƙasurgumin shugaban yan ta'addan Boko Haram a wani hari a jihar Borno.
An samu asarar rayuka mutanen da ba su ji ba, ba su gani ba yayin da wasu miyagun ƴan bindiga, suka kai mummunan farmaki kan wasu ƙauyuka a jihar Taraba.
Wasu miyagun yan bindiga sun kai hari a jihar Zamfara inda suka halaka mutum biyu har lahira. Ƴan bindigan sun kai sabon farmakin ne a garin Kauran-Namoda.
Aikin ceto da dakarun sojoji karkashin jagorancin Manjo Janar Godwin Mutkut suka yi a jihar Sokoto ya yi sanadiyar ceto mutum 31 da aka yi garkuwa da su.
Hukumar makarantar Jami'ar Usman Dan Fodio ta karyata jita-jitar cewa 'yan bindiga sun kai hari cikin makarantar tare da hallaka wani mutum daya.
Wasu 'yan bindiga sun sace matar dagaci a kauyen Ruwandorawa da ke jihar Zamfara bayan sun bindige wani dan sanda da kuma sace wasu mutane 15 a kauyen.
Wasu mutane da ake zargin yan ta'addan Boko Haram ne sun kashe yan sanda biyu tare da raunata wasu a ayarin motoccin Gwamna Mai Mala Buni na Jihar Yobe.
Wasu miyagun ƴan bindiga sun kai farmaki a jihar Kaduna inda suka halaka wani baban fasto na cocin Evangelical Church Winning All (ECWA) da sace matarsa.
Mayakan ISWAP da Boko Haram akalla 60 ne su ka hallaka yayin wani artabu tsakaninsu a tsibirin Tumbum Ali da ke karamar hukumar Marte a cikin jihar Borno.
Yan ta'adda
Samu kari