Peter Obi Y bada Mamaki Ya Halarci Kaddamar Kamfe na Wani Dan Takarar Shugaban Kasa a 2027

Peter Obi Y bada Mamaki Ya Halarci Kaddamar Kamfe na Wani Dan Takarar Shugaban Kasa a 2027

  • Dan takarar shugaban kasa na NDC, Peter Obi, ya halarci taron kaddamar da yakin neman zaben dan takarar APM, Gwamna Seyi Makinde
  • Obi ya isa wajen taron da misalin karfe 12.31 na rana yayin da ke dana da fara yakin neman zaben Gwamna Makinde na jihar Oyo
  • Har yanzu ba a bayyana dalilin da ya sa Peter Obi ya halarci taron ba yayin da ake ci gaba da gudanar da shi a yau Litinin, 7 ga Satumba, 2026

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Oyo, Nigeria - Dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar NDC, Peter Obi, ya halarci taron kaddamar da yakin neman zaben dan takarar APM a zaben shugaban kasa na 2027, Seyi Makinde.

Rahotanni sun nuna cewa Obi, tsohon gwamnan jihar Anambra, ya isa wajen taron da misalin karfe 12.31 na rana yau Litinin, 7 ga watan Satumba, 2026.

Kara karanta wannan

2027: Jam'iyyar NDC ta su Kwankwaso ta fitar da sunayen yan takarar gwamna a jihohi 12

Gwamna Makinde da Obi.
Dan takarar shugaban kasa na APM kuma gwamnan Oyo, Seyi Makinde da Peter Obi Hoto: Seyi Makinde, Peter Obi
Source: Twitter

Jaridar Tribune Nigeria ta ruwaito cewa har yanzu ba a bayyana manufarsa ta halartar taron ba yayin da ake ci gaba da gudanar da shi.

Ana sa ran Makinde zai kaddamar da ofishin yakin neman zabensa a matsayin wani bangare na shirye-shiryen taron.

Cikakken bayani na nan tafe…

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262