Peter Obi Y bada Mamaki Ya Halarci Kaddamar Kamfe na Wani Dan Takarar Shugaban Kasa a 2027
- Dan takarar shugaban kasa na NDC, Peter Obi, ya halarci taron kaddamar da yakin neman zaben dan takarar APM, Gwamna Seyi Makinde
- Obi ya isa wajen taron da misalin karfe 12.31 na rana yayin da ke dana da fara yakin neman zaben Gwamna Makinde na jihar Oyo
- Har yanzu ba a bayyana dalilin da ya sa Peter Obi ya halarci taron ba yayin da ake ci gaba da gudanar da shi a yau Litinin, 7 ga Satumba, 2026
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Oyo, Nigeria - Dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar NDC, Peter Obi, ya halarci taron kaddamar da yakin neman zaben dan takarar APM a zaben shugaban kasa na 2027, Seyi Makinde.
Rahotanni sun nuna cewa Obi, tsohon gwamnan jihar Anambra, ya isa wajen taron da misalin karfe 12.31 na rana yau Litinin, 7 ga watan Satumba, 2026.

Kara karanta wannan
2027: Jam'iyyar NDC ta su Kwankwaso ta fitar da sunayen yan takarar gwamna a jihohi 12

Source: Twitter
Jaridar Tribune Nigeria ta ruwaito cewa har yanzu ba a bayyana manufarsa ta halartar taron ba yayin da ake ci gaba da gudanar da shi.
Ana sa ran Makinde zai kaddamar da ofishin yakin neman zabensa a matsayin wani bangare na shirye-shiryen taron.
Cikakken bayani na nan tafe…
Asali: Legit.ng