An Yi Amfani da Ramadan, Malaman Musulunci Sun Yi Addu'a domin Tazarcen Tinubu
- Wata kungiyar ‘yan kasuwa, 'Iyaloja General Movement', ta shirya addu’a na musamman domin Bola Ahmed Tinubu a zaben 2027
- Taron da aka yi a Lagos ya samu halartar sarakuna, malamai, shugabannin kasuwa da magoya bayan jam'iyyar APC
- Kungiyar ta kuma raba tallafin abinci ga mabukata domin rage radadin da ake ciki a lokacin azumin watan Ramadan mai alfarma
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Ikeja, Lagos - Wata kungiya mai suna 'Iyaloja General Movement' ta shirya zaman addu’a domin shugaba Bola Tinubu da gwamnatinsa a Najeriya.
Kungiyar ta shirya addu'o'in ne domin neman nasarar sake zaben shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, a babban zaben shekarar 2027.

Source: Facebook
An yi addu'o'i ga Bola Tinubu a Lagos
An gudanar da taron ne a Lagos, inda ya samu halartar sarakuna, malamai na addinin Musulunci, shugabannin kasuwa da sauran masu ruwa da tsaki a siyasa, cewar Punch.
Haka kuma, magoya bayan jam’iyyar APC da shugabannin al’umma daga sassa daban-daban sun halarci taron domin nuna goyon bayansu.
Taron ya kasance wani bangare na laccar Ramadan ta shekara ta tara da kuma addu’o’i na musamman da kungiyar ke shiryawa duk shekara.
Har ila yau, an gudanar da rabon tallafin abinci domin taimaka wa mabukata a lokacin azumin Ramadan.

Source: Facebook
Sarakuna da suka halarci taron a Lagos
Daga cikin sarakunan da suka halarci taron akwai Oba Kamila Isiba, Olu na Agege sai Oba Ambaliu Adegbeyi, Alaige na Orile Agege da Oba Latif Egbeyemi, Ologba na Ogba.
Mai kula da kungiyar, Mutiullahi Oladeebo, ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da aka fitar, cewar New Telegraph.
Ya ce taron na daga cikin kokarin kungiyar na goyon bayan sake zaben Tinubu saboda irin jagorancin da yake yi.
Oladeebo ya ce kungiyar na ganin cewa matakan da shugaban kasa ke dauka za su taimaka wajen bunkasa ci gaban kasa.
Musabbabin taron addu'ar da aka yi
A cewarsa, taron ya kuma zama gangamin farkon da kungiyar za ta yi domin goyon baya ga shugaban kasa da sauran ‘yan takarar jam’iyyar a zabe mai zuwa.

Kara karanta wannan
Hadimin Osinbajo ya raba wa ADC gardama, ya fadi mutum 2 da suka dace da yin takara a 2027
Ya ce sun taru ne a cikin watan Ramadan domin neman taimakon Allah ga shugabannin kasar.
Ya kara da cewa a matsayin Musulmai suna da yakinin cewa Allah yana karbar addu’a musamman a cikin watan Ramadan mai alfarma.
A karshe, ya bayyana kwarin gwiwa cewa APC da ‘yan takararta za su samu nasara a zabe mai zuwa duba da ayyukan alheri da suke yi a kasa.
Dan ADC ya yi magana da Legit Hausa
Muhammad Salisu ya nuna damuwarsa kan yadda al'umma suka dawo kan zabe.
Ya ce abin takaici ne saboda dan abin da mutum zai samu ya manta da halin da ake ciki a kasa.
A cewarsa:
"Muna fama da tsadar rayuwa da rashin tsaro amma wasu suna neman sayar da rayuwarsu."
Ya shawarci yan Najeriya da su yi taka tsantsan saboda wannan ita ce dama ta karshe.
Limami ya yi wa Tinubu addu'a a masallaci
An ji cewa babban limami a masallacin kasa, Farfesa Luqman Zakariyah ya yi wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu addu'o'i bayan sallar Juma'a.
Limamin ya yi wa shugaban kasa addu'ar samun nasara a mulkinsa yayin daura auren 'ya'yan karamin ministan tsaro, Bello Matawalle.
Ya kuma roki Allah Madaukakin Sarki da ya sanya albarka a cikin wadannan aurarraki da aka daura, ya ba ma’auratan zaman lafiya a rayuwarsu ta aure.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng

