Cikakkun Jerin Jihohin da ke Karkashin Ikon APC, PDP Bayan Zabukan Kogi, Bayelsa da Imo

Cikakkun Jerin Jihohin da ke Karkashin Ikon APC, PDP Bayan Zabukan Kogi, Bayelsa da Imo

Aisha Musa ta shafe tsawon shekaru tana kawo labaran Hausa a bangaren siyasa, tsegumi da al’amuran yau da kullum

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Al'ummar jihohin Imo, Kogi da Bayelsa sun yi tururuwan fitowa a ranar Asabar, 11 ga watan Nuwamba domin zaben yan takarar da suke muradi a matsayin gwamnoninsu.

Bayan kammala zabe da tattara sakamako, Gwamna Hope Uzodimma na APC ya sake zarcewa a karo na biyu a jihar Imo, haka kuma Gwamna Duoye Diri na PDP a jihar Bayelsa.

An yi sabbin gwamnoni bayan zabukan Imo, Bayelsa da Kogi
Cikakkun Jerin Jihohin da ke Karkashin Ikon APC, PDP Bayan Zabukan Kogi, Bayelsa da Imo Hoto: Hope Uzodimma/Alahaji Usman Ododo/Douye Diri
Asali: Facebook

Alhaji Usman Ododo na APC shine ya lashe zaben gwamna a jihar Kogi kuma za a rantsar da shi a watan Janairun 2024 bayan cikar wa'adin mulkin Gwamna Yahaya Bello.

Bayan kammala zabukan ciko na gwamnoni, ga jerin jihohi da jam'iyyar APC mai mulki, PDP, Labour Party da sauransu ke iko a cikinsu.

Kara karanta wannan

Dalilai 4 da suka sa Anyanwu na PDP ya fadi zaben gwamnan Imo na 2023

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kudu maso Gabas

Alex Otti (Abia) Labour Party

Dan takarar jam'iyyar Labour Party mai shekaru 58 ya samu gagarumin nasara a zaben gwamna da aka gudanar a ranar 16 ga watan Maris.

Tsohon Manajan Darakta na Bankin Diamond ya sha kaye a zaben gwamnan a 2015 da 2019, Channels TV ta rahoto.

Francis Nwifuru (Ebonyi): APC

Nwifuru ya kasance kakakin majalisar dokokin jihar Ebonyi sau biyu. Mutumin mai shekaru 48 ya fito ne daga Oferekpe Agbaja a karamar hukumar Izzi ta jihar.

Peter Mbah (Enugu) PDP

Da siyasar mai shekaru 51, shi ne wanda ya kafa kuma shugaban kamfanin Pinnacle Oil and Gas Ltd. Ya kuma kasance lauya kuma mai sharhi kan harkokin kudi. Ya fito daga Owo a karamar hukumar Nkanu ta Gabas

Hope Uzodimma (Imo) APC

Kara karanta wannan

Hukuncin kotun daukaka kara: Farfesan arewa ya yi gargadi kan yiwuwar barkewar rikici a Kano

Ya kasance sanata mai wakiltan Imo ta Yamma tsakanin 2011 da 2019.

Charles Soludo (Anambra) APGA

Dan siyasar mai shekaru 63 ya kasance ma'aikacin banki kuma farfesa a fannin tattalin arziki a jami'ar Najeriya.

Soludo ya kasance tsohon gwamna kuma shugaban kwamitin gudanarwa na babban bankin Najeriya.

Kudu maso Kudu

Umo Eno (Akwa Ibom) PDP

Dan siyasar mai shekaru 59 ya yi aiki a matsayin kwamishinan filaye da albarkatun ruwa na jihar Akwa Ibom.

Bassey Otu (Cross River) APC

Ya kasance tsohon dan majalisar wakilai wanda ya wakilci Calabar Municipal/Odukpan kuma Sanata mai wakiltar Cross River ta Kudu.

Sheriff Oborevwori (Delta): PDP

Tsohon kakakin majalisar dokokin jihar Delta daga 2017 zuwa 2023. Dan siyasar mai shekaru 60 ya wakilci mazabar Okpe yayin da yake majalisa.

Siminalayi Fubara (Rivers): PDP

Fubara ya kasance tsohon akanta janar na jihar Rivers. Gwamnan ya fito ne daga Garin Opobo a karamar hukumar Opobo/Nkoro.

Kara karanta wannan

INEC ta mika satifiket ga sabon gwamnan APC, ya tura muhimmin sako

Godwin Obaseki (Edo) PDP

Obaseki ya kasance Shugaban tawagar Tattalin Arziki da Dabaru ta Jihar Edo a karkashin gwamnatin Adams Oshiomhole.

Ya yi aiki a matsayin mamba na kwamitin zartarwa na kamfanoni masu zaman kansu da dama ciki har da Afrinvest.

Douye Diri (Bayelsa) PDP

Dan siyasar mai shekaru 64, ya kasance sanata mai wakiltar Bayelsa ta tsakiya daga 2019 zuwa 2020 a majalisar dokokin tarayya ta 9.

Kudu maso yamma

Babajide Sanwo-Olu (Lagos) APC

Dan siyasar mai shekaru 57 ya kasance tsohon shugaban hukumar raya kadarori na jihar Legas.

Dapo Abiodun (Ogun): APC

Dan siyasar mai shekaru 62, shi ne ya kafa kamfanin First Power Limited kuma ya yi aiki a matsayin manajan darakta na Heyden Petroleum.

Abiodun shi ne tsohon shugaban hukumar kula da harkokin kamfanoni (CAC).

Seyi Makinde (Oyo) PDP

Gwamnan mai shekaru 55 ya kafa kamfanin Makon Engineering and Technical Services (METS) a lokacin yana da shekaru 29 a cikin 1997

Kara karanta wannan

Dalilai 3 da suka sa Timipre Sylva na APC ya sha kaye a zaben gwamnan Bayelsa

Ya fadi zaben gwamna a 2015 a karkashin jam’iyyar Social Democratic Party (SDP)

Rotimi Akeredolu (Ondo) APC

Gwamnan mai shekaru 67, ya kasance babban Lauyan Najeriya (SAN) kuma tsohon shugaban kungiyar lauyoyin Najeriya (NBA) a shekarar 2008.

Abiodun Oyebanji (Ekiti) APC

Dan siyasar mai shekaru 56 ya kasance tsohon sakataren gwamnatin jihar Ekiti kuma tsohon shugaban ma'aikata.

Ademola Adeleke (Osun) PDP

Gwamnan mai shekaru 63 ya kasance tsohon Sanata mai wakiltar Osun ta Yamma daga 2017 zuwa 2019 a Majalisar Tarayya Abuja.

Arewa ta Tsakiya

Rabaran Hyacinth Alia (Benue) APC

An zabi limamin cocin katolikan a ranar 19 ga watan Maris karkashin jam'iyyar APC mai mulki.

Dan siyasar mai shekaru 49 a duniya ya kasance dan majalisar wakilai a shekarar 2011. Ya kammala karatunsa a jami’ar Fasaha ta Tarayya ta Minna. ya shafe shekaru a matsayin ma’aikacin banki kafin ya shiga harkokin siyasa.

Caleb Mutfwang (Plateau): PDP

Kara karanta wannan

Filato: Gabannin hukuncin kotun daukaka kara, malamin addini ya yi gagarumin gargadi ga Gwamna

Gwamnan jihar Filato mai ci a yanzu ya kasance dan siyasa ne mai shekaru 58. Mutfwang ya kasance tsohon shugaban karamar hukumar Mangu.

AbdulRahman AbdulRazaq (Kwara): APC

Kafin nasararsa a shekarar 2015, dan siyasar mai shekaru 63 ya sha kaye a zaben gwamna tsakanin 2007 da 2011 a karkashin jam'iyyar Congress for Progressive Change (CPC).

Abdullahi Sule (Nasarawa) APC

Wanda ya kafa kamfanin mai na Sadiq Petroleum Nigeria Limited kuma daga baya ya zama shugaban kamfanin African Petroleum (AP) Plc a shekarar 2001.

An nada shi Babban Manajan Darakta na kamfanin sikari na Dangote kafin ya zama gwamna a 2019.

Zababben gwamna Usman Ododo (Kogi) APC

Gogaggen ma'aikacin bankin shi ne tsohon babban mai binciken kananan hukumomi.

Ododo zai karbi ragamar mulki daga hannun gwamna mai ci Yahaya Bello, wanda ya fito daga jam’iyyar APC mai mulki.

Arewa maso Yamma

Umar Namadi (Jigawa): APC

Kara karanta wannan

Wasu sun sace wayar tsohon minista a kotu wajen sauraron shari’ar zabe

Akantan ya kasance tsohon mataimakin gwamna kuma wanda ya assasa kamfanin Namadi, Umar & Co.

Shi ne shugaban sashen kula da asusun rukunin kamfanonin Dangote.

Uba Sani (Kaduna): APC

Tsohon sanatan Kaduna ta tsakiya kuma mataimakin shugaban masu faftukar dimokradiyya na kasa (Arewa).

Gwamnan mai shekaru 52 ya karbi ragamar mulki daga hannun Mallam Nasir El-Rufai.

Abba Yusuf (Kano): NNPP

Dan siyasar mai shekaru 60 ya kasance tsohon kwamishinan ayyuka, gidaje da sufuri. Injiniyan shine gwamnan NNPP na farko a Najeriya.

Dikko Radda (Katsina) APC

Dan siyasar mai shekaru 53 ya kasance tsohon sakataren walwala na APC na kasa, ya kuma taba rike mukamin darakta-janar na hukumar SMEDAN kafin ya karbi mulki daga hannun Aminu Masari.

Nasir Idris (Kebbi) APC

Gwamnan mai shekaru 57 a duniya shi ne shugaban kungiyar malamai na Najeriya. Idris ya kuma kasance mataimakin shugaban kungiyar kwadago ta Najeriya.

Kara karanta wannan

Zabe ya kammala a Kogi, INEC ta sanar da wanda ya lashe zabe, ya fi kowa adadin kuri'u

Ahmad Aliyu (Sokoto): APC

Aliyu tsohon mataimakin gwamna ne kuma kwamishina a jihar Sokoto. Gwamnan mai shekaru 53 ya kuma yi aiki a matsayin babban akanta a ma’aikatar kula da ayyukan kananan hukumomi da kuma babban sakataren hukumar yan sanda.

Dauda Lawal (Zamfara): PDP

Gwamnan mai shekaru 57, ya kasance tsohon gwamnan babban bankin kasa, mai ba Lamido Sanusi shawara na musamman kan harkokin bankin Musulunci.

Gogaggen ma’aikacin bankin ya yi digirin digirgir a fannin kasuwanci a Jami’ar Usmanu Danfodiyo da ke Sakkwato.

Arewa ta Gabas

Kefas Agbu (Taraba): PDP

Dan siyasar mai shekaru 52, ya kasance Laftanar kanar na soja mai ritaya.

Agbu ya kasance tsohon shugaban hukumar gudanarwar na NIMASA kuma mamba a kwamitin shugaban kasa kan shirin Arewa maso Gabas (2016-2019).

Ahmadu Fintiri (Adamawa) PDP

Gwamnan mai shekaru 55 ya rike mukamin mukaddashin gwamna daga watan Yuli zuwa Oktoban 2014 a lokacin da aka tsige Gwamna Murtala Nyako.

Kara karanta wannan

PDP ta lshe karamar hukuma ta farko yayin da INEC ta fara tattara sakamakon karshe a Bayelsa

Kafin wannan lokacin, Fintiri ya kasance kakakin majalisar dokokin jihar Adamawa.

Bala Mohammed (Bauchi) PDP

Gwamnan mai shekaru 64, ya kasance tsohon ministan babban birnin tarayya (FCT) kuma Sanata mai wakiltar Bauchi ta Kudu a majalisar dokokin kasar.

Mohammed ya kuma yi aiki a matsayin Babban Jami’in Gudanarwa a Fadar Shugaban Kasa daga 1994 zuwa 1995.

Babagana Zulum (Borno) APC

Zulum ya kasance Farfesa kuma tsohon shugaban riko na tsangayar aikin injiniya a jami'ar Maiduguri.

Inuwa Yahaya (Gombe) APC

Gwamnan mai shekaru 61, ya taba rike mukamin kwamishinan kudi da bunkasa tattalin arziki.

Inuwa yayi aiki a matsayin manajan darakta na kamfanin A.Y.U Civil Engineering Company Ltd kafin ya shiga harkar siyasa a shekarar 1999.

Mai Mala Buni (Yobe) APC

Dan siyasar mai shekaru 55, shine zababben sakataren jam’iyyar APC na kasa na farko.

Buni ya kuma zama shugaban riko na jam’iyyar (2020-2022) bayan korar Adam Oshiomhole.

Kara karanta wannan

Abubuwa 7 da su ka taimaki APC, suka Kashe LP da PDP a zaben Gwamnan Imo

Kotu ta tsige gwamnan Filato

A wani labarin kuma, mun ji cewa kotun daukaka kara ta gabatar da hukunci a shari’ar zaben gwamnan Filato wanda ya gudana a farkon shekarar nan ta 2023.

Leadership ta rahoto cewa Alkalan kotun daukaka kara sun tabbatar da jam’iyyar APC ce ta lashe zaben gwamnan jihar na Filato.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng