Majalisar Dokokin Ogun Ta Karbi Sunayen Kwamishinoni 10 da Gwamna Ya Nada

Majalisar Dokokin Ogun Ta Karbi Sunayen Kwamishinoni 10 da Gwamna Ya Nada

  • Gwamna Dapo Abiodun na jihar Ogun ya tura ƙarin sunayen mutum 10 da ya naɗa kwamishinoni zuwa majalisar dokoki
  • Majalisar ta tabbatar da zuwan sunayen, kuma ta fara shirye-shiryen fara tantance su ranar Laraba, 13 ga watan Satumba
  • Tun bayan rantsar da shi, gwamna Abiodun ya aika sunayen kwamishinoni 8 zuwa majalisa kuma har yau bai rantsar da su ba

DUBA NAN: Bibiyi shafin Legit.ng Hausa a kafar TikTok. Kada ka bari bidiyo mai daukar hankali ya wuce ka!

Jihar Ogun - Majalisar dokokin jihar Ogun ta karɓi jerin sunayen ƙarin kwamishinoni 10 daga mai girma gwamna Dapo Abiodun na jam'iyyar APC.

Magatakardan majalisar, Mista Deji Adeyemo, shi ne ya tabbatar da haka a wata sanarwa da ya rattaɓa wa hannu ranar Talata, kamar yadda Channels tv ta ruwaito.

Majalisar dokokin jihar Ogun.
Majalisar Dokokin Ogun Ta Karbi Sunayen Kwamishinoni 10 da Gwamna Ya Nada Hoto: pmnews
Asali: Twitter

Sanarwan ta nuna cewa mambobin majalisar dokokin za su fara aikin tantance mutanen da gwamnan ya naɗa ranar Laraba (Yau) 13 ga watan Satumba, 2023 daga ƙarfe 2:00 na rana zuwa abinda ya sawwaƙa.

Kara karanta wannan

Dubu Ta Cika: An Kama Malamin Da Ya Damfari Wata Baiwar Allah Kuɗi Sama da Naira Miliyan 1.6

Jerin sunayen sabbin kwamishinon da za a tantance

Legit Hausa ta tattaro muku jerin sunayen sabbin kwamishinonin da majalisar zata tantance, ga su kamar haka;:

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

1. Honorabul Adeleye-Oladapo Adijat

2. Injiniya Taiwo Oludotun

3. Mista Sofela Adebola Emmanuel

4. Honorabul Ilori-Oduntan Olufemi

5. Injiniya Dairo Oluwagbenga

6. Honorabul Owootomo Bolu

7. Mista Oresanya Oladimeji

8. Honorabul Balogun Ademola

9. Mista Osunbiyi Tunde

10. Mista Fagbayi Sesan.

Bugu da ƙari, sanarwan ta umarci waɗanda aka naɗa su kai kwafin takardun karatunsu da sauran bayanansu ga ofishin magatakardan majalisa da misalin ƙarfe 10:00 na safiyar Laraba.

Kwamishinoni na wa gwamnan ya naɗa zuwa yanzu?

Jaridar PM News ta tattaro cewa gwamna Dapo Abiodun na jihar Ogun ya naɗa kwamishinoni 8 ne kacal tun bayan karɓan rantsuwar kama aiki a zango na biyu.

Kara karanta wannan

Sanatan APC Ya Lallasa Jam'iyyar PDP da LP, Kotun Zaɓen NASS Ta Yanke Hukunci

Idan baku manta ba, a watan Yuli, 2023 gwamnan ya tura sunayen kwamishinoni Takwas ga majalisar dokokin kuma tuni aka tantance su amma har yanzu ba a rantsar da su ba.

Adamawa: Ban Taba Aje Biliyan Daya a Asusun Banki Ba a Matsayin Gwamna, Ngilari

A wani labarin kuma Tsohon Gwamnan Adamawa ya tabbatar da cewa bai taɓa samun kuɗin da suka kai Naira biliyan ɗaya ba a asusunsa har ya gama mulki.

A kwanakin bayan an ji Bala Ngilari na cewa zai iya faɗuwa ya suma idan ya ga kuɗi Biliyan N1bn a cikin asusun bankinsa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262