Cikakken Jerin Ministocin da Ake Tsammanin Tinubu Zai Nada Gabanin 28 Ga Yuli

Cikakken Jerin Ministocin da Ake Tsammanin Tinubu Zai Nada Gabanin 28 Ga Yuli

Tun daga ranar da ya karbi mulkin Najeriya, shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya fara iki ba kama hannun yaro kuma ya jure wa duk wata matsin lamba da ta biyo bayan wasu matakan da ya ɗauka.

Ayyukan da shugaba Tinubu ya fara yi daga shiga ofis ya sa 'yan Najeriya suka ƙara ɗora tsammani kan sabon shugabansu kuma tuni aka fara zancen su wa zai naɗa Ministoci, The Cable ta ruwaito.

Shugaba Najeriya, Bola Ahmed Tinubu.
Cikakken Jerin Ministocin da Ake Tsammanin Tinubu Zai Nada Gabanin 28 Ga Yuli Hoto: Bola Ahmed Tinubu
Asali: Facebook

Meyasa ya zama wajibi Tinubu ya gabatar da sunayen Ministoci gabanin ranar 28 ga watan Yuli, 2023?

A halin yanzun, shugaba Tinubu ba zai tsaya iya nan ba kuma ana tsammanin zai fitar da jerin sunayen Minstocinsa daga nan zuwa ranar 28 ga watan Yuli, 2023, saboda daga ranar ya cika watanni 2 a Ofis.

Kara karanta wannan

Shugaba Bola Tinubu Ya Shiga Ganawar Sirri da Asari Dakubo a Aso Villa, Bayanai Sun Fito

Sabuwar dokar da tsohon shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, ya rattaɓa wa hannu ta nuna duk sabon shugaban da ya zo, yana da watanni 2, watau kwanaki 60 ya miƙa sunayen ministoci ga majalisa.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Matukar Tinubu bai yi wa wannan doka garambawul ba, ana ganin zai miƙa sunayen Ministoci 27 daga yanzu zuwa ranar 28 ga watan Yuli mai zuwa.

Jerin ministocin da Shugaba Tinubu zai naɗa

1. Ministan birnin tarayya Abuja

2. Ministan noma da raya karkara

3. Ministan harkokin sufurin jiragen sama a Najeriya

4. Ministan Kasafin kudi da tsare-tsaren ƙasa

5. Ministan kasuwanci da masana'antu

6. Ministan ilimi

7. Ministan mahalli

8. Ministan kuɗi

9. Ministan lafiya

10. Ministan yaɗa labarai da al'adu

11. Ministan sadarwa da tattalin arzikin zamani

12. Ministan harkokin cikin gida

13. Ministan shari'a

14. Ministan kwadugo da samar da ayyukan yi

Kara karanta wannan

Manyan Jiga-Jigai 2 Sun Gana da Shugaba Tinubu a Villa, Sun Yi Bayani Mai Jan Hankali

15. Ministan albarkatun man fetur

16. Ministan albarkatun ruwa

17. Ministan harkokin mata da walwala

18. Ministan ma'adanan ƙasa da ƙarafa

19. Ministan tsaro

20. Ministan Neja Delta

21. Ministan wutar lantarƙi

22. Ministan sufuri

23. Ministan ayyukan jin ƙai, Ibtila'i da walwalar al'umma

24. Ministan kimiyya da fasaha da kirkire-kirkire

25. Ministan matasa da wasanni

26. Ministan ayyuka da gidaje

27. Ministan harkokin waje.

Idan baku manta ba a makon da ya shiga, shugaba Tinubu ya tura wasiƙa ga majalisar dattawa, yana neman ta sahale masa ya naɗa masu ba da shawara 20.

Jerin Jihohin da Shugaba Tinubu Zai Gamu da Ciwon Kai Yayin Zaɓo Ministoci da Dalilai

A wani labarin kuma mun kawo muku jerin sunayen jihohin da shugaba Tinubu zai iya fama wajen zaɓo wanda zai naɗa a matsayin minista.

Mafi karanci, ana hasashen shugaban ƙasan zai sha wahala wajen zaɓo Ministoci a jihohi 4 saboda jam'iyyar APC ta sha kashi a zaben gwamna da Sanatoci a jihohin.

Kara karanta wannan

Karin Bayani: Shugaba Tinubu Ya Sa Labule da Tsohon Sarkin Kano, Sanusi Lamido, Bayanai Sun Fito

Asali: Legit.ng

Online view pixel