Zaben Gwamnoni: Jerin Jihohin Da PDP Ka Iya Lallasa APC Da Sauran Jam’iyyu a Cikinta

Zaben Gwamnoni: Jerin Jihohin Da PDP Ka Iya Lallasa APC Da Sauran Jam’iyyu a Cikinta

A ranar 18 ga watan Maris ne yan Najeriya a jihohi mabanbanta za su fita rumfunar zabe domin zabar yan takarar da za su jagorance su a matsayin gwamnoni na tsawon shekaru hudu masu zuwa.

Za a gudanar da zabukan gwamnonin ne a fadin jihohi 28 daga cikin 36 na Najeriya.

Wasu daga cikin masu neman takarar gwamnoni a inuwar PDP
Zaben Gwamnoni: Jerin Jihohin Da PDP Ka Iya Lallasa APC Da Sauran Jam’iyyu a Cikinta Hoto: BBC News
Asali: UGC

A wannan zauren. Legit.ng Hausa ta jeranto maku wasu jihohi da ake ganin babbar jam'iyyar adawar kasar ta Peoples Democratic Party (PDP) zata iya lashewa a zabukan gwamnonin masu zuwa.

Kamar yadda hasashen kungiyoyin Enough is Enough (EiE) da SB Morgen (SBM) suka nuna, jam'iyyar PDP na iya lashe jihohi 15 a zabe mai zuwa.

Ga rin jihohin da ake ganin PDP za ta iya yin nasara a zabukan gwamnonin

  1. Sokoto
  2. Kebbi
  3. Oyo
  4. Katsina
  5. Kaduna
  6. Bauchi
  7. Gombe
  8. Adamawa
  9. Cross River
  10. Akwa Ibom
  11. Rivers
  12. Delta
  13. Taraba
  14. Ebonyi
  15. Plateau

Kara karanta wannan

Zaben gwamnoni: Jihohi 28 ne za a yi zabe gobe Asabar, ga jerin sunayensu

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Zabukan gwamnoni sun fi na shugaban kasa rikitarwa, NSA Monguno

A wani labari na daban, babban mai ba kasa shawara a kan lamarin tsaro, Manjo Janar Babagana Monguno, ya bayyana cewa zabukan gwamnoni da za a yi a ranar 18 ga watan Maris, zai fi na shugaban kasa da aka yi rikitarwa.

Sai dai kuma, Monguno wanda ya bayyana hakan a ranar Talata, 15 ga watan Maris, ya ce basa hango kowani rikici ko hargitsi da ke kawo kai ko zai tarwatsa tsarin a yan kwanaki masu zuwa.

Duk da haka, ya ce shugaban ma'aikatan tsaro da sufeto janar na yan sanda wadanda sune kan gaba a tsarin tsaron zaben suna ta ganawa don tabbatar da an yi zaben cikin kwanciyar hankali da lumana.

Yakubu Dogara ya ayyana goyon bayansa ga dan takarar gwamnan APC a Bauchi

Kara karanta wannan

Zaben Gwamnoni: Jerin Jihohi 10 Da APC Za Ta Iya Lallasa PDP Da Sauran Jam'iyyu

A wani lamarin kuma, tsohon kakakin majalisar wakilai, Yakubu Dogara ya ayyana goyon bayansa ga dan takarar gwamna na jam'iyyar APC a jihar Bauchi, Air Marshal Sadiqque Baba Abubakar mai ritaya gabannin zabe.

Dogara ya bayyana cewa dan takarar PDP a zaben kuma gwamna mai ci, Bala Mohammed bai yi wani abun a zo a gani a jihar ba don haka ya bukaci al'ummar jihar da su tsige shi a zabe mai zuwa.

Asali: Legit.ng

Online view pixel