Zababbun Sanatoci Sun Karbi Takardar Shaidar Cin Zabe Daga Wajen INEC a Abuja

Zababbun Sanatoci Sun Karbi Takardar Shaidar Cin Zabe Daga Wajen INEC a Abuja

  • Yan majalisa da aka zabe a zaben majalisar dokokin tarayya da ya gudana a ranar Asabar, 25 ga watan Fabrairu sun karbi takardar shaidar cin zabensu
  • Hukumar zabe ta kasa mai zaman kanta (INEC) ce ta gabatarwa yan majalisar da wadannan satifiket din
  • An gabatarwa zababbun sanatocin da satifikets dinsu ne a cibiyar taro ta kasa da kasa da ke Abuja

Abuja - A ranar Asabar, 25 ga watan Fabrairu ne yan Najeriya suka je rumfunar zabe don zabar yan majalisar da za su wakilci mazabunsu a matakin kasa.

An ayyana wasu daga cikin sanatocin da aka zaba a matsayin wadanda suka lashe zabe nan take yayin da aka ayyana wadanda zabukan yankinsu bai kammalu ba daga baya.

INEC na gabatarwa zababbun sanatoci takardar shaidar cin zabe
Zababbun Sanatoci Sun Karbi Takardar Shaidar Cin Zabe Daga Wajen INEC a Abuja Hoto: INEC
Asali: Twitter

Wata wallafa da hukumar zabe ta kasa mai zaman kanta (INEC) ta yi ya nuna cewa an mikawa zababbun sanatocin takardun shaidar cin zabensu a cibiyar kasa da kasa da ke Abuja a ranar Talata, 7 ga watan Maris.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Wasu daga cikin yan takarar da suka yi nasarar zuwa majalisar dattawa ta Goma sun hada da Orji Uzor-Kalu wanda ke wakiltan Abia ta kudu, da Ahmad Lawan wanda a yanzu haka shine shugaban majalisar dattawa ta tara. Lawan zai wakilci Yobe ta arewa.

Har ila yau, yayin da INEC ta saki jerin sunayen wadanda aka zaba a majalisar wakilai, ba a baiwa wadannan yan majalisar takardar shaidar cin zabensu ba.

INEC ta cire sunan Doguwa cikin zababbun yan majalisar wakilai

A gefe guda, mun ji cewa hukumar zabe ta kasa mai zaman kanta, INEC, ta cire sunan Alhassan Ado Doguwa na jihar Kano daga cikin wadanda suka yi nasara a zaben majalisar wakilai na 2023.

Da farko INEC ta ayyana Doguwa a matsayin wanda ya yi nasara a zabe sai dai kuma ko sama ko kasa ba a ga sunansa ba a cikin jerin sunayen zababbun yan majalisa da aka saki a ranar Talata.

Kamar yadda hukumar ta sanar, ta ce an matsawa baturen zaben yankin wajen ayyana Doguwa a matsayin wanda ya lashe zaben dan majalisar wakilai mai wakiltan mazabar Doguwa/Tudun Wada a jihar Kano.

Jam'iyyar PDP ta ce lallai Atiku ne ya ci zabe ba Tinubu ba

A wani labari na daban, jam'iyyar PDP ta yi watsi da ayyana Asiwaju Bola Tinubu a matsayin zababben shugaban kasa, ta ce lallai dan takararta, Atiku Abubakar ne ya ci zabe.

Asali: Legit.ng

Online view pixel