Atiku Abubakar Ya Bayyana Tsawon Lokacin Da Zasu Kwashe Suna Zanga-Zanga

Atiku Abubakar Ya Bayyana Tsawon Lokacin Da Zasu Kwashe Suna Zanga-Zanga

  • Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam'iyyar PDP, Atiku Abubakar ya bayyana lokacin da zasu kwashe suna zanga-zangar da suke yi
  • Jam'iyyar PDP dai ta fara gudanar da zanga-zanga domin nuna adawa da sakamakon zaɓen shugaban ƙasa wanda jam'iyyar APC ta samu nasara
  • Atiku Abubakar ya kuma tabbatar da cewa duk da zanga-zangar da suke yi, za kuma su je kotu domin neman haƙƙin su

Abuja- Dan takarar kujerar shugaban ƙasa a ƙarƙashin inuwar jam'iyyar Peoples Democratic Party (PDP), Atiku Abubakar, a ranar Litinin ya bayyana cewa jam'iyyar zata cigaba da zanga-zangar da take yi kullum har na tsawon lokaci.

Atiku, wanda yayi magana lokacin da ya jagoranci zanga-zangar da jam'iyyar take yi zuwa hedikwatar hukumar INEC, yace zanga-zangar ba zata hana su zuwa kotu ba domin ƙalubalantar sakamakon zaɓen shugaban ƙasar. Rahoton The Nation

Kara karanta wannan

An Dakatar da Shugaban Jam'iyyar APC a Neja Bisa Zargin Dangwalawa Atiku Kuri'a

Zanga-zanga
Atiku Abubakar Ya Bayyana Tsawon Lokacin Da Zasu Kwashe Suna Zanga-Zanga Hoto: The Nation
Source: UGC

Jam'iyyar ta kuma miƙa takardar koke ga hukumar zaɓen mai zaman kanta ta ƙasa (INEC).

Barr. Festus Okoye, kwamishin labarai da wayar da kan masu kaɗa ƙuri'a na ƙasa na hukumar shine ya amshi takardar.

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

Atiku ya jagoranci sauran shugabannin jam'iyyar domin nuna adawar su kan sakamakon zaɓen shugaban ƙasa wanda jam'iyyar All Progressives Congress (APC), ta lashe.

“Muna yin zanga-zanga sannan muna da dukkanin ƴancin yin zanga-zanga. Duk da cewa muna zanga-zanga hakan ba zai dakatar da mu daga zuwa kotu ba. Zamu yi zanga-zanga mai tsawo. Ko kullum ko duk bayan kwana ɗaya.

Sauran waɗanda suke a cikin masu zanga-zangar akwai shugaban jam'iyyr na ƙasa, Dr. Iyorchia Ayu, tsohon shugaban jam'iyyar na ƙasa, Prince Uche Secondus; gwamnan jihar Sokoto Aminu Tambuwal. Rahoton Daily Post

Sauran sun haɗa da tsohon shugaban majalisar dattawa, Bukola Saraki; Kola Ologbondiyan, Daniel Bwacha, sanata Dino Melaye da sauran su.

Kara karanta wannan

Goyon Bayan Tinubu: Ɗan Takarar Gwamnan Labour Party Na Ruwa, Jam'iyyar Na Shirin Juya Masa Baya

Dan Shekara 27 Daga Arewa Ya Ajiye Tarihin Zama ‘Dan Autan ‘Yan Majalisar Tarayya

A wani labarin na daban kuma, wani matashi ɗan Arewacin Najeriya, ya kafa sabon tarihi a majalisar wakilai ta Najeriya.

Matashin wanda ya fito daga jihar Ƙebbi ya kafa wannan tarihin ne a.zaɓen da ya gabata.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng