Sanatan PDP Ya Ba Buhari Uzuri, Ya Fadi Inda Aka Samu Matsala a Gwamnatin APC

Sanatan PDP Ya Ba Buhari Uzuri, Ya Fadi Inda Aka Samu Matsala a Gwamnatin APC

  • Danjuma La’ah yana ganin Muhammadu Buhari ya samu matsala ne daga wadanda ke zagaye da shi
  • Sanatan na PDP ya ce wadanda aka ba mukamai ba suyi abin da ya kamata, kuma ba a duba aikinsu
  • La’ah ya bayyana abin da ya hana shi komawa APC duk da jam’iyyar ta mamaye yankin da ya fito

Abuja – Sanata Danjuma La’ah ya yi hira da jaridar Punch a kan zamansa a majalisar dattawa, siyasar Najeriya da kuma salon gwamnatin APC mai-ci.

Danjuma La’ah ne shugaban marasa rinjaye a majalisa, shi kadai ne Sanatan jam’iyyar PDP daga yankin Muhammadu Buhari na Arewa maso yamma.

Sanatan yake cewa duk da jam’iyyar APC tayi karfi a shiyyarsa, bai sauya sheka daga PDP ba.

“Ban ga dalilin sauya-sheka ba. Zan iya tunawa shugaban kasa da kan shi ya tambaye ni meyasa ba zan shiga APC ba, na fada masa ina kare martabar PDP ne.”

Kara karanta wannan

Tinubu ga 'yan Kaduna: Ni na san yadda zan kawo karshe 'yan bindiga, ku zabe ni na gaji Buhari

Akwai kuskuren da ‘yan Najeriya ke yi a halin da ake ciki. Dole mutum ya yi hattara da kashe-kashen da ake yi, idan mutum yana adawa, babu mai goyon bayansa."

- Danjuma La’ah

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

La'ah v Nasir El-Rufai

Sanatan adawan ya zargi Gwamna Nasir El-Rufai da yin bakin kokarinsa na ganin ya hana shi zuwa majalisar dattawa, amma bai yi nasara a kansa ba.

La’ah yake cewa saboda Nasir El-Rufai yana Gwamna, babu yadda ya iya da abin da ake yi a majalisa, musamman idan Sanata yana yi wa jama’ansa aiki.

Buhari
Shugaban Najeriya Hoto: @BashirAhmaad
Asali: Twitter

Har ila yau, Sanatan na Kudancin Kaduna ya zargi wasu Gwamnonin da yin watsi da wasu bangarorin jihohinsu musamman wadanda ba su zabe su ba.

Rikicin gidan PDP

A game da rikicin PDP, ‘dan siyasar bai ganin cewa lamarin zai kawo masu cikas a zabe mai zuwa, yace burinsu shi ne yadda za a kai Atiku/Okowa ga nasara.

Kara karanta wannan

Yadda APC da LP Ke Tsara Dabarun Hana Jam’iyyar NNPP Kai Labari a Jihar Kano

An rahoto shi yana cewa Atiku Abubakar da Ifeanyi Okowa sun yi bakin kokarinsu wajen tallata manufofinsu, amma duk da haka wasu ba za su zabe su ba.

Gwamnatin Buhari

Da aka yi masa tambaya a kan mulkin Buhari, La’ah ya ce a ra’ayinsa shugaban kasar yana da niyya mai kyau, amma bai yi dace da mukarabbai a mulkinsa ba.

A cewarsa ba a duba aikin da wadanda aka ba mukamai suke yi, kuma ba a yin kokari wajen ganin an tabbatar wadanda aka nada, sun yi abin da ake bukata.

A cikin 100%, ‘dan majalisar na Kudancin Kaduna ya ce zai ba gwamnatin Buhari 50% zuwa 60%.

Siyasar 2023

Kun samu rahoto a Gwamnonin Arewa maso yamma da ke barin mulki, Aminu Tambuwal da Atiku Bagudu ne kurum za su shiga takarar Majalisar Dattawa.

Nasir El-Rufai, Abdullahi Ganduje, Badaru Abubakar da Aminu Masari ba su cikin ‘Yan takara a 2023, shi kuma Bello Matawalle ne zai nemi tazarcen Gwamna.

Kara karanta wannan

Ina Tinubu Ya Ga Kafasitin Da Zai Mulki Nigeria, Yaje Ya Huta Kawai Inji PDP

Asali: Legit.ng

Online view pixel