Saboda Barin Baya Mai Kyau, Na Yi Ayyuka Masu Tasiri Barkatai

Saboda Barin Baya Mai Kyau, Na Yi Ayyuka Masu Tasiri Barkatai

  • Shugaba Buhari na Najeriya ya bayyana kadan daga ayyukan da gwamnatinsa ta yi kuma masu tasiri cikin kankanin lokaci
  • Shugaban ya kuma yaba da cewa, aikin da gwamnatinsa ta yi zai zama tarihin da za a ke tunawa a Najeriya
  • Nan da watanni kasa da shida shugaban kasa Muhammadu Buhari zai bar mulki, bayan zaben 2023 da za a yi

FCT, Abuja - Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yaba da irin ayyukan da gwamnatinsa ta yi masu tasiri a bangarori daban-daban na kasar nan, jaridar TheCable ta ruwaito.

Shugaban ya bayyana hakan ne a lokacin da yake magana a taron waiwaye ga ayyukan ministocinsa da aka shirya don duba makomar ajandoji tara na gwamnatinsa.

Buhari ya ce ya yi ayyukan da 'yan Najeriya ke alfahari dasu
Saboda Barin Baya Mai Kyau, Na Yi Ayyuka Masu Tasiri Barkatai | Hoto: premiumtimesng.com
Asali: UGC

Da yake magana a taron a ranar Litinin, Buhari ya bayyana kadan daga nasarorin da gwamnatinsa ta samu a fannin ayyukan more rayuwa, noma, tattalin arziki da lafiya.

Kara karanta wannan

Abinda Yasa Nake Da Gwarin Guiwar Cewa Ni Zan Lashe Zaben Shugaban Kasa a 2023, Tinubu Ya Magantu

Kadan daga ayyukan da Buhari ya yi

Ya kuma bayyana cewa, gwamnatinsa ta samu nasarar gina hanyoyin da nisansu ya kai kilomita 3,800 a fadin kasar nan.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Buhari ya ce, gwamnatinsa ta samar da sabbin jiragen sama ga sojin sama don samun sauki wajen kawo karshen rashin tsaro.

A bangare guda, ya ce gwamnatinsa ta yi nasarar kammala aikin layin dogon Itakpe-Ajaokuta-Warri, kamar yadda jaridar People Gazette ta ruwaito.

Hakazalika, ya ce wadannan ayyuka sun samu ne ta hanyar tallafi daga NNPC da kamfanin Dangote da ma wasu cibiyoyi a kasar nan.

Idan baku manta ba, kasa da shekara guda ne ya saura wa shugaba Buhari ya sauka daga mulki, a karshen wa'adinsa na biyu.

Tinubu Ya Gaji, Kamata Yayi Ya Koma Gida Ya Yi Hutawarsa, Inji Na Hannun Daman Atiku

A wani labarin, jigon jam'iyyar PDP Phrank Shaibu ya caccaki dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu.

Kara karanta wannan

"Ita Ta Nemeni Da Soyayya": Dan Jarida Makaho Yayi Tsokaci Kan Aure da rayuwarsa

A wata sanarwa da ya aikewa Legit.ng a jiya Lahadi 16 ga watan Oktoba, Shaibu ya bayyana cewa, duba da lafiyar Tinubu, bai cancanci ya gaji shugaban kasa Buhari ba.

Ya kuma bayyana cewa, Tinubu ya sha kwabsawa a maganganunsa tun bayan da ayyana aniyarsa ta zama shugaban kasa, wanda hakan ke nuna a rude yake gaba daya.

Asali: Legit.ng

Online view pixel