Lawan, Ekweremadu, Gbaja da Sanatoci da ‘Yan Majalisan da suka fi kowa dadewa a Majalisa
- A siyasar Duniya, a kan samu ‘yan siyasan da suka shafe shekara da shekaru su na aikin majalisa
- ‘Yan majalisa ba su da wa’adi, za su iya daukar tsawon rayuwarsu a kan kujera idan har sun ci zabe
- A Najeriya akwai ‘yan majalisar tarayyar da sun yi fiye da shekaru 20 su na wakiltar mazabunsu
ABIN LURA: Za ku iya ceton rayuwar diya mace dake cikin hadari. Bada gudunmuwarka ga Patreon na Legit
1. Nicholas Mutu
Tun da aka dawo mulkin farar hula a shekarar 1999, Hon. Nicholas Mutu ne yake wakiltar mutanen Bomadi/Patani na jihar Delta a majalisar tarayya.
Nicholas Mutu ya rike shugabancin kwamitin Neja-Delta tun daga 2009 zuwa 2019. Punch ta ce shi ya fi kowane ‘dan majalisa yawan ayyuka na NDDC.
2. Ahmad Lawan
A zaben 1999 ne Ahmad Ibrahim Lawan ya zama ‘dan majalisar yankin Bade/Jakusko. A wannan kujera ne ya yi shekaru takwas a ANPP har zuwa 2007.

Kara karanta wannan
Wasu ‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mahaifiyar ‘dan takaran Sanatan Kano cikin dare
A zaben na 2007 ne Dr. Ahmad Lawan ya zama Sanatan Arewacin jihar Yobe. Tun lokacin nan ya zama Sanata, a 2019 ya karbi iko da majalisar dattawan.
DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar
3. Femi Gbajabiamila
Rt. Hon. Femi Gbajabiamila shi ne shugaban majalisar wakilan tarayya na kasa a yau. ‘Dan siyasar yana kan wa’adinsa na biyar kenan a kujerar majalisa.
A 2003 Femi Gbajabiamila ya zama ‘dan majalisar yankin Surulere I, tun wancan lokaci bai fadi zabe ba. Bayan shekara 16 ya zama mutum na hudu a kasar.
4. Muhammad Ali Ndume
Shi ma Muhammad Ali Ndume ya zama ‘dan majalisar wakilai na yankin Chibok/Damboa/Gwoza ne a 2003, ya yi shekara takwas yana rike da wannan mukami.
A 2011 aka zabe shi a matsayin Sanatan kudancin Borno, har yau kuma shi ne a kan kujerar.
5. Ike Ekweremadu
Ba a taba yin wanda ya dade yana jagorantar majalisar dattawa kamar Sanata Ike Ekweremadu ba. Shi ma ya zo majalisa ne a 2003, kuma ya dade ana yi da shi.

Kara karanta wannan
Na hango nasara ne, shiyasa na rabu da Saraki, na bi layin Atiku a PDP inji Dino Melaye
Ike Ekweremadu ya shafe shekaru 12 a jere a matsayin mataimakin shugaban majalisar dattawa.

Asali: UGC
6. James Manager
Ba zai yiwu ayi maganar Santaocin da suka dade ba tare da an ambaci James Manager. Sanatan zai cika shekara 20 yana wakiltar mutanen kudancin Delta a 2023.
7. Leo Ogor
Wani ‘dan siyasa da ya tare a majalisar tarayya tun 2003 shi ne Leo Ogor. A shekara mai zuwa ‘dan majalisar na Isoko-North/Isoko-South zai cika shekara 20.
8. Alhassan Ado-Doguwa
Shugaban masu rinjaye a majalisar wakilai, Alhassan Ado-Doguwa ya zo majalisa ne a 2007. Ana tunanin yana harin shugaban majalisa idan ya zarce a 2023.
9. Mohammed Monguno
Wani wanda ya dade a majalisa kuma yana neman shugabanci shi ne Hon. Mohammed Monguno mai wakiltar Marte/Monguno/Nganzai, sau biyar ana rantsar da shi.
10. Kabiru Ibrahim Gaya
A shekarar 2007 ne Kabiru Ibrahim Gaya ya zama Sanatan kudancin Kano a majalisar dattawa. A zabe mai zuwa shi ne zai sake tsayawa jam’iyyar APC takara a Kano.

Kara karanta wannan
Takarar Tinubu, Osinbajo, Amaechi da Lawan a 2023 ta na raba kawunan na-kusa da Buhari
11. Enyinnaya Abaribe
Bayan rikicinsa da Gwamnansa a 2007, Enyinnaya Abaribe ya zama Sanatan Abia ta kudu a majalisa, shekararsa 15 kenan bai motsa daga majalisar dattawan ba.
12. Yakubu Dogara
Tsohon shugaban majaliar wakilai, Yakubu Dogara yana cikin wadanda suka ga jiya da yau a majalisa, tun 2007 yake wakiltar Bogoro, Dass da Tafawa Balewa.
13. Mukhtar Betara
Wani ‘dan majalisan Borno a jerin shi ne mai wakiltar mazabun Biu/Bayo/Shani, a 2007 Mukhtar Betara ya zo majalisa, kuma babu mamaki ya zarce har 2027.
14. Khadijah Abba-Ibrahim
Babu macen da ta dade a majalisa kamar Khadijah Abba-Ibrahim mai wakiltar Damaturu/Gujba/Gulani/Tarmuwa, sau biyar ta na cin zabe a yankinta a Yobe.
PDP ta shiga rudu a Legas
Akwai shirin gudanar da wani sabon zaben fitar da gwani da jam’iyyar PDP ta ke yi a jihar Legas. Idan za a tuna, dazu mu ka fitar maku da wannan labarin.
A yau ake tunanin za a zabi wadanda za su yi wa PDP takarar ‘yan majalisa a jihar Legas bayan rusa zaben ‘yan takarar majalisar tarayya da aka yi a Mayu.
Asali: Legit.ng