Lawan, Ekweremadu, Gbaja da Sanatoci da ‘Yan Majalisan da suka fi kowa dadewa a Majalisa

Lawan, Ekweremadu, Gbaja da Sanatoci da ‘Yan Majalisan da suka fi kowa dadewa a Majalisa

  • A siyasar Duniya, a kan samu ‘yan siyasan da suka shafe shekara da shekaru su na aikin majalisa
  • ‘Yan majalisa ba su da wa’adi, za su iya daukar tsawon rayuwarsu a kan kujera idan har sun ci zabe
  • A Najeriya akwai ‘yan majalisar tarayyar da sun yi fiye da shekaru 20 su na wakiltar mazabunsu

ABIN LURA: Za ku iya ceton rayuwar diya mace dake cikin hadari. Bada gudunmuwarka ga Patreon na Legit

1. Nicholas Mutu

Tun da aka dawo mulkin farar hula a shekarar 1999, Hon. Nicholas Mutu ne yake wakiltar mutanen Bomadi/Patani na jihar Delta a majalisar tarayya.

Nicholas Mutu ya rike shugabancin kwamitin Neja-Delta tun daga 2009 zuwa 2019. Punch ta ce shi ya fi kowane ‘dan majalisa yawan ayyuka na NDDC.

2. Ahmad Lawan

A zaben 1999 ne Ahmad Ibrahim Lawan ya zama ‘dan majalisar yankin Bade/Jakusko. A wannan kujera ne ya yi shekaru takwas a ANPP har zuwa 2007.

Kara karanta wannan

Wasu ‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mahaifiyar ‘dan takaran Sanatan Kano cikin dare

A zaben na 2007 ne Dr. Ahmad Lawan ya zama Sanatan Arewacin jihar Yobe. Tun lokacin nan ya zama Sanata, a 2019 ya karbi iko da majalisar dattawan.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

3. Femi Gbajabiamila

Rt. Hon. Femi Gbajabiamila shi ne shugaban majalisar wakilan tarayya na kasa a yau. ‘Dan siyasar yana kan wa’adinsa na biyar kenan a kujerar majalisa.

A 2003 Femi Gbajabiamila ya zama ‘dan majalisar yankin Surulere I, tun wancan lokaci bai fadi zabe ba. Bayan shekara 16 ya zama mutum na hudu a kasar.

4. Muhammad Ali Ndume

Shi ma Muhammad Ali Ndume ya zama ‘dan majalisar wakilai na yankin Chibok/Damboa/Gwoza ne a 2003, ya yi shekara takwas yana rike da wannan mukami.

A 2011 aka zabe shi a matsayin Sanatan kudancin Borno, har yau kuma shi ne a kan kujerar.

5. Ike Ekweremadu

Ba a taba yin wanda ya dade yana jagorantar majalisar dattawa kamar Sanata Ike Ekweremadu ba. Shi ma ya zo majalisa ne a 2003, kuma ya dade ana yi da shi.

Kara karanta wannan

Na hango nasara ne, shiyasa na rabu da Saraki, na bi layin Atiku a PDP inji Dino Melaye

Ike Ekweremadu ya shafe shekaru 12 a jere a matsayin mataimakin shugaban majalisar dattawa.

Hon. Femi Fbajabiamila
Shugaban Majalisar Wakilai, Rt. Hon. Femi Fbajabiamila Hoto: premiumtimesng.com
Asali: UGC

6. James Manager

Ba zai yiwu ayi maganar Santaocin da suka dade ba tare da an ambaci James Manager. Sanatan zai cika shekara 20 yana wakiltar mutanen kudancin Delta a 2023.

7. Leo Ogor

Wani ‘dan siyasa da ya tare a majalisar tarayya tun 2003 shi ne Leo Ogor. A shekara mai zuwa ‘dan majalisar na Isoko-North/Isoko-South zai cika shekara 20.

8. Alhassan Ado-Doguwa

Shugaban masu rinjaye a majalisar wakilai, Alhassan Ado-Doguwa ya zo majalisa ne a 2007. Ana tunanin yana harin shugaban majalisa idan ya zarce a 2023.

9. Mohammed Monguno

Wani wanda ya dade a majalisa kuma yana neman shugabanci shi ne Hon. Mohammed Monguno mai wakiltar Marte/Monguno/Nganzai, sau biyar ana rantsar da shi.

10. Kabiru Ibrahim Gaya

A shekarar 2007 ne Kabiru Ibrahim Gaya ya zama Sanatan kudancin Kano a majalisar dattawa. A zabe mai zuwa shi ne zai sake tsayawa jam’iyyar APC takara a Kano.

Kara karanta wannan

Takarar Tinubu, Osinbajo, Amaechi da Lawan a 2023 ta na raba kawunan na-kusa da Buhari

11. Enyinnaya Abaribe

Bayan rikicinsa da Gwamnansa a 2007, Enyinnaya Abaribe ya zama Sanatan Abia ta kudu a majalisa, shekararsa 15 kenan bai motsa daga majalisar dattawan ba.

12. Yakubu Dogara

Tsohon shugaban majaliar wakilai, Yakubu Dogara yana cikin wadanda suka ga jiya da yau a majalisa, tun 2007 yake wakiltar Bogoro, Dass da Tafawa Balewa.

13. Mukhtar Betara

Wani ‘dan majalisan Borno a jerin shi ne mai wakiltar mazabun Biu/Bayo/Shani, a 2007 Mukhtar Betara ya zo majalisa, kuma babu mamaki ya zarce har 2027.

14. Khadijah Abba-Ibrahim

Babu macen da ta dade a majalisa kamar Khadijah Abba-Ibrahim mai wakiltar Damaturu/Gujba/Gulani/Tarmuwa, sau biyar ta na cin zabe a yankinta a Yobe.

PDP ta shiga rudu a Legas

Akwai shirin gudanar da wani sabon zaben fitar da gwani da jam’iyyar PDP ta ke yi a jihar Legas. Idan za a tuna, dazu mu ka fitar maku da wannan labarin.

A yau ake tunanin za a zabi wadanda za su yi wa PDP takarar ‘yan majalisa a jihar Legas bayan rusa zaben ‘yan takarar majalisar tarayya da aka yi a Mayu.

Kara karanta wannan

Wasu Makusanta da Mukarraban Shugaban kasa 7 da suka gagara samun takara a APC

Asali: Legit.ng

Online view pixel