2023: Mataimakin gwamnan Katsina ya yi murabus daga mukaminsa, zai yi takarar gwamna
- Gabannin zaben 2023, mataimakin gwamnan jihar Katsina, Mannir Yakubu, ya sauka daga mukamin kwamishinan noma
- Yakubu ya yi murabus daga kujerar ne domin ya shiga fafutukar neman takarar kujerar gwamnan jihar a zabe mai zuwa
- Wannan mataki da ya dauka ya biyo bayan umurnin da Gwamna Aminu Bello Masari ya bayar na cewa duk masu neman takara su sauka daga mukamansu
Katsina - Mataimakin gwamnan jihar Katsina, QS Mannir Yakubu, ya yi murabus daga mukaminsa na kwamishinan noma a yayin da yake shirye-shiryen kaddamar da aniyarsa ta son yin takarar kujerar gwamna a zaben 2023.
Labarin murabus din nasa na kunshe ne a cikin wata sanarwa da babban sakataren labaransa, Ibrahim Musa Kallah, ya saki a daren ranar Talata, Vanguard ta rahoto.
![2023: Mataimakin gwamnan Katsina ya yi murabus daga mukaminsa, zai yi takarar gwamna 2023: Mataimakin gwamnan Katsina ya yi murabus daga mukaminsa, zai yi takarar gwamna](https://cdn.legit.ng/images/1120/002e0b7d9e11ab04.jpeg?v=1)
Asali: UGC
A cewar sanarwar, wannan hukunci nasa ya yi daidai da sashi 84 (12) na dokar zaben 2022 kamar yadda aka gyara ta.
![](https://cdn.legit.ng/images/360x203/ae5f16b9be11e9d6.jpeg?v=1)
Kara karanta wannan
Zulum ya yi rabon buhuhunan hatsi, kudi da atamfa ga mutum 100,000 a cikin garin Maiduguri da Jere
Dokar ta bukaci duk masu rike da mukaman siyasa da ma’aikatan gwamnati dake neman yin takara a zabe su yi murabus daga mukamansu.
Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!
Mataimakin gwamnan a cikin jawabin ya yi godiya ga Allah da Gwamna Aminu Masari kan dama da ya bashi na ci gaba da bayar da gudunmawa wajen dawo da harkar noma a jihar karkashin mulkinsa.
Mannir ya kuma nuna jin dadinsa kan sake fasalin bangaren noma inda manoman suka samu sauyi wajen noma wanda ke tabbatar da tsaron abinci da bukatun noma a jihar da ma Najeriya baki daya, rahoton PM News.
Sanata mai wakiltan yankin Buhari ya sauya sheka daga APC zuwa PDP a hukumance
A wani labarin, Ahmed Babba Kaita, sanata mai wakiltan yankin Katsina ta arewa, wato mazabar shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a hukumance.
![](https://cdn.legit.ng/images/360x203/59d09eb3442c02d8.jpeg?v=1)
Kara karanta wannan
Bidiyon yadda Ganduje ya kalli Wike ido cikin ido ya fada masa cewa ba zai kai labari ba a 2023
Premium Times ta rahoto cewa Mista Babba-Kaita ya sanar da cewa ya koma jam’iyyar People’s Democratic Party (PDP) mai adawa, a ranar Laraba, 20 ga watan Afrilu.
Sauya shekar nasa ya kawo karshen rade-radin da ake ta yi a gidajen radiyo a Katsina da kuma shafukan soshiyal midiya cewa sanatan zai sauya jam’iyyar siyasa gabannin babban zaben 2023.
Asali: Legit.ng