Kwankwaso, tsohon ministan Buhari: Jerin yan siyasar da suka kafa sabuwar kungiyar siyasa

Kwankwaso, tsohon ministan Buhari: Jerin yan siyasar da suka kafa sabuwar kungiyar siyasa

Abuja – Gabannin babban zaben 2023, an kafa wata sabuwar kungiyar siyasa da ke neman karbe mulki daga hannun jam’iyyun All Progressives Congress (APC) da Peoples Democratic Party (PDP).

Tsohon gwamnan jihar Kano, Rabiu Kwankwaso ne ya sanar da kafa sabuwar kungiyar siyasar mai suna ‘The National Movement (TNM)’ a babban cibiyar taro ta kasa da ke Abuja, a ranar Talata, 22 ga watan Fabrairu.

Kwankwaso, tsohon ministan Buhari: Jerin yan siyasar da suka kafa sabuwar kungiyar siyasa
Kwankwaso, tsohon ministan Buhari: Jerin yan siyasar da suka kafa sabuwar kungiyar siyasa Hoto: @KKSY_Reporters
Asali: Twitter

Ga jerin yan siyasar da suka halarci taron kaddamar da sabuwar kungiyar:

1. Rabiu Kwankwaso

Tsohon gwamnan jihar Kano, Rabiu Kwankwaso, ya kasance jigon jam'iyyar PDP har zuwa lokacin da ya sanar da kafa sabuwar kungiyar.

Kara karanta wannan

Abubuwa 10 da Kwankwaso ya fada wajen kaddamar da sabuwar tafiyar siyasarsu

A jawabansa na baya ya bayyana cewa APC da PDP basu da wani abun nunawa yan Najeriya a 2023.

Kwankwaso ya sha yunkurin zama shugaban kasa amma bai cimma nasara ba.

2. Sanata Suleiman Hunkuyi

Sanata Suleiman Hunkuyi ya wakilci Kaduna ta arewa a majalisar dokokin tarayya ta takwas. Ya bar APC zuwa PDP gabannin zaben 2019.

Ya yi takarar tikitin gwamna na jam'iyyar PDP amma ya sha kaye a hannun Isa Ashiru.

3. Solomon Dalung

Solomon Dalung ya rike mukamin ministan matasa da wasanni a karkashin gwamnatin Muhammadu Buhari ta farko.

Yana daya daga cikin ministocin da basu samu damar komawa majalisar Buhari ta biyu ba bayan sake zabarsa.

4. Buba Galadima

Buba Galadima ya kasance na hannun damar shugaba Buhari kafin alakarsu ta yi tsami gabannin zaben 2019.

5. Idris Wada

Idris Wada ya kuma kasance jigon PDP sannan tsohon gwamnan jihar Kogi.

Kara karanta wannan

Ko PDP ta so, ko ta ki, sai APC ta lashe zaben 2023: Mataimakin Shugaban Majalisar dattawa

Sauran manyan yan Najeriya da suka hallara a wajen sanar da sabuwar kungiyar sune:

6. Tanko Yakasai

7. Air Vice Marshall Ifeanaju

8. Solomon Edoda

9. Nweze Onu

10. Falasade Aliyu

11. Rufai Alkali

12. Grace Ben

13. Umale Shittu

14. Ibrahim Ringim

15. Ali Gwaska

16. Paul Okala

17. Rufai Hanga

18. Abdulrahman Abubakar, da sauransu.

Duk da sun kafa TMN, Kwankwaso ya na nan daram-dam-dam a jam’iyyar PDP

A gefe guda, mun ji cewa Rabiu Musa Kwankwaso wanda shi ne jagoran sabuwar tafiyar siyasa ta The National Movement a Najeriya, ya yi karin haske kan inda suka sa gaba.

Sanata Rabiu Kwankwaso a wata hira da ya yi da BBC Hausa, ya tabbatar da cewa bai sauya-sheka daga jam’iyya PDP kamar yadda wasu mutane ke tunani ba.

Kwankwaso ya ce The National Movement kungiya ce ba jam’iyyar siyasa ba, wanda suka kafa domin ganin an fitar da Najeriya daga halin da take ciki a yanzu.

Kara karanta wannan

Mun fi karfin mataimakin shugaban kasa, dole a ba mu kujerar shugaban kasa - Kungiyar Ibo

Asali: Legit.ng

Online view pixel