Akwai Kura: Bayan Shekara 12, Kamfanin Uber Ya Dakatar da Ayyukansa a Najeriya
- Uber ya sanar da cewa zai kawo ƙarshen ayyukansa a Najeriya daga 2 Metaga Satumba 2026, bayan ya shafe sama da shekaru 12 yana aiki a ƙasar.
- Kamfanin ya fara aiki a Legas a shekarar 2014, inda ya ce ya ji daɗin kasancewa cikin rayuwar yau da kullum ta masu amfani da manhajarsa
- Shugaban Uber, Dara Khosrowshahi, ya kuma sanar da rage ma’aikata kusan kashi 10 cikin 100, kwatankwacin mukamai 3,300
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
Legas, Najeriya - Shahararren kamfanin jigilar fasinjoji, Uber, ya sanar da dakatar da ayyukansa a Najeriya.
Kamfanin na Uber ya sanar da cewa zai dakatar da ayyukansa ne daga ranar Laraba, 2 ga watan Satumban 2026.

Source: Getty Images
Kamfanin Uber ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ya fitar, inda ya ce ya yanke wannan hukunci ne bayan gudanar da cikakken nazari kan ayyukansa a ƙasar, cewar rahoton jaridar Daily Trust.
Uber ya fara gudanar da ayyukansa a Najeriya ne a shekarar 2014, lokacin da ya fara aiki a birnin Legas.
Uber ya yi bankwana da masu amfani da shi
Kamfanin Uber ya bayyana cewa dakatar da ayyukansa zai fara aiki daga ranar 2 ga Satumba 2026.
Uber ya ce:
“Muna rubuto wannan saƙo ne domin sanar da ku wani labari mai wahala. Bayan cikakken nazari kan harkokin kasuwancinmu, mun yanke shawarar kawo ƙarshen ayyukanmu a Najeriya daga 2 ga Satumba 2026.”
Kamfanin ya ce tun lokacin da ya fara aiki a Legas a shekarar 2014, ya ɗauki kasancewarsa wani ɓangare na rayuwar yau da kullum ta ’yan Najeriya a matsayin babban abu.
Ya ce manhajar ta taimaka wajen haɗa mutane da direbobin da ke ba da hidimar sufuri mai zaman kanta, jaridar The Punch ta kawo labarin.
Kamfanin Uber ya yi godiya
Uber ya kuma gode wa masu amfani da manhajar bisa amincewarsu da kamfanin wajen haɗa su da direbobi domin isa wuraren da suke son zuwa cikin aminci, jaridar The Punch ta kawo labarin.
Kamfanin ya amince cewa matakin na iya kawo cikas ga tsarin zirga-zirgar masu amfani da shi, sannan ya nemi afuwar waɗanda za su fuskanci matsala sakamakon ficewarsa daga Najeriya.

Source: Getty Images
Uber ya sanar da sallamar ma’aikata 3,300
A wani lamarin kuma, kamfanin Uber ya sanar da cewa zai rage yawan ma’aikatansa da kusan kashi 10 cikin 100, wanda ya yi daidai da kusan mukamai 3,300.
Shugaban kamfanin na Uber, Dara Khosrowshahi, ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ya aikewa ma’aikatan Uber ranar Laraba.
Direban Uber ya cinye abinci
A wani labarin kuma, kun ji cewa wata matashiyar 'yar Najeriya ta bayar da bayani kan yadda ta kaya tsakanin kawarta da wani direban Uber.
Dirama ya barke bayan kawarta ta tura direban Uber ya karbo mata abincin Sallah daga wajen wata kawarta.
Direban Uber din ya gaggauta kawo karshen tafiyar tasa, sannan ya sace abincikin tare da tura sakon ban hakuri bayan ya cinye abincin.
Asali: Legit.ng

