Likitocin Najeriya Sun Shiga Yajin Aiki, Za Su Rufe Asibitocin Gwamnati Baki 1
- Kungiyar likitoci masu neman kwarewar aiki (NARD) ta sanar da shiga yajin aikin sai baba ta gani daga ranar Talata, 7 ga Afrilu, 2026
- Likitocin sun dauki wannan matakin ne bayan da gwamnatin tarayya ta dakatar da biyan alawus-alawus da aka amince musu a baya
- Idan har aka fara wannan yajin aikin a ranar Talata, dubban marasa lafiya a manyan asibitocin gwamnati za su kasance cikin garari
Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida.
Abuja – Sashin lafiya na Najeriya na shirin fuskantar gagarumin kalubale bayan da kungiyar likitoci masu neman kwarewar aiki (NARD) ta sanar da shiga yajin aikin sai-baba-ta-gani.
Matakin shiga yajin aikin ya fito ne bayan wani taron gaggawa na majalisar zartarwa ta kungiyar (NEC) da aka gudanar ta yanar gizo a ranar Asabar, 4 ga Afrilu, 2026.

Source: Twitter
Likitoci sun sanar da shiga yajin aiki
Babban sakataren kungiyar, Shuaibu Ibrahim, ya bayyana cewa yajin aikin zai fara ne da misalin karfe 12:00 na safiyar ranar Talata, 7 ga Afrilu, 2026, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.
Ya siffanta matakin gwamnatin tarayya na dakatar da tsarin alawus din kwararru (PAT) a matsayin abin takaici da zai jefa rayukan marasa lafiya cikin hadari.
Rikicin ya samo asali ne daga yarjejeniyar da aka kulla tsakanin NARD da gwamnatin tarayya bayan wani dogon yajin aiki da aka yi a shekarar 2025.
Yarjejeniyar ta tanadi karin kudaden alawus na zuwa aiki, aikin dare, da kuma alawus din tura likitoci zuwa karkara domin inganta jin dadin su.
Duk da cewa an fara aiwatar da wannan tsarin a watan Fabrairu, NARD ta zargi gwamnati da shirin dakatar da biyan kudaden a watan Afrilu.
Wannan mataki ya girgiza amintar da ke tsakanin bangarorin biyu, inda likitocin ke ganin gwamnati ta karya alkawarin da ta dauka na gyara bangaren lafiya yau.
Bukatu 7 na likitoci ga gwamnati
Kungiyar NARD ta bukaci gwamnati ta gaggauta janye shawarar dakatar da tsarin PAT tare da biyan daukacin kudaden da ake bin ta bashi.
Shuaibu Ibrahim ya jaddada cewa dole ne a biya ragowar albashin wasu cibiyoyin lafiya da kuma kudaden horar da likitoci na shekarar 2026 (MRTF) ba tare da bata lokaci ba.
Haka kuma, kungiyar tana neman a biya bashin alawus na kwararru da ya kai na tsawon watanni 19 dake makale a hannun gwamnati, in ji rahoton Punch.
Likitocin sun bukaci mambobinsu a fadin jihohin kasar nan da su kasance tsintsiya madaurinki daya har sai an cimma nasarar da ake bukata domin ci gaban aikin lafiya.

Source: Getty Images
Tasirin yajin aikin ga marasa lafiya
Idan har aka fara wannan yajin aikin a ranar Talata, dubban marasa lafiya a manyan asibitocin gwamnati za su kasance cikin garari.
Wannan na faruwa ne a daidai lokacin da kasar ke kokarin farfadowa daga kalubalen lafiya daban-daban, wanda hakan zai iya tsananta halin da asibitoci ke ciki yau.
A halin yanzu, kungiyar ta ce ba za ta koma bakin aiki ba har sai gwamnati ta nuna alamun gaskiya wajen cika alkawuranta yau.
Wata malamar jinya a Maiduguri, jihar Borno, Zainab Nafiu, ta shaidawa Legit Hausa cewa ita da take tare da likitocin NARD, ta san irin kokarin da suke yi sosai a wajen kula da marasa lafiya.
Zainab Naifu ta ce:
"Gaskiya suna kokari, don kowane lokaci ka shiga asibiti sai ka tarar da su, kuma komai dare, sai ka samu wadanda ke aikin dare.
"Duk da cewa dama suna neman kwarewar aiki ne, amma marasa lafiya sun fi samun kulawa daga gare su fiye daga asalin manyan likitoci.
"Maganar tafiya yajin aikinsu, ina ganin ba karamar matsala zai zama ba. Ka ga ko a kwanakin baya, sun je yajin aikin nan, kuma ba a ji da dadi ba, don haka bai kamata a ce gwamnati tana wasa da rayukan marasa lafiya ba."
Zainab Nafiu ta roki gwamnati da ta yi mai yiwuwa wajen ganin likitocin ba su shiga wannan yajin aiki ba, wanda a cewarta zai iya jawo mace macen marasa lafiya saboda rashin samun kulawar da suke bukata.
'Yan Najeriya na kukan tsadar jinya
A wani labari, mun ruwaito cewa, Yajin aikin kungiyar likitoci ta NARD ya fara jefa mutane marasa lafiya cikin wahala musamman masu karamin karfi.
Rahoto ya nuna cewa mutane sun fara karkata zuwa asibitocin kudi domin samun kulawa amma suna kuka kan tsadar kudin jinya.
Kungiyar NARD ta tsunduma yajin aiki ne a ranar Asabar, 1 ga watan Nuwamba, 2025 kuma ta ce ba za ta janye ba sai an biya bukatunta.
Asali: Legit.ng



