Yakin Amurka, Isra'ila da Iran Ya Taba Najeriya, Farashin Litar Fetur Ya Haura N1350

Yakin Amurka, Isra'ila da Iran Ya Taba Najeriya, Farashin Litar Fetur Ya Haura N1350

  • Litar man fetur ta kusa kai ₦1,400 a sassan Najeriya sakamakon tashin farashin danyen mai a kasuwar duniya saboda rikicin Amurka, Isra'ila da Iran
  • Direbobin motocin kasuwa a Legas da Kano sun koka kan yadda yanzu ba sa samun riba, yayin da matafiya ke fama da tsadar kudin sufuri a kasar
  • Wasu da aka zanta da su, sun bayyana irin radadin da suke ji game da wannan karin kudin, wanda ake fargabar zai ci gaba da tashi a nan gaba

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Ci gaba da tashin farashin man fetur ya ƙara tsananta radadin tattalin arziki a faɗin Najeriya, inda a yanzu farashin lita ɗaya ya kusa kai ₦1,400 a wurare da dama.

Wannan lamari ya jefa direbobi, matafiya, da masu sana'o'i cikin fargaba sakamakon yadda farashin danyen mai a kasuwar duniya yake tashi.

Kara karanta wannan

Makamin da Iran ta harba ya keta tsaron Isra'ila, ya fada kusa da cibiyar nukiliya

Yakin Amurka da Iran ya jawo farashin fetur ya karu sosai a Najeriya.
Wasu masu ababen hawa na sayen man fetur a gidan man NNPCL. Hoto: Bloomberg/Contributor
Source: Getty Images

Farashin litar fetur ta kai kusan ₦1,400

Binciken jaridar Daily Trust a manyan birane ya nuna cewa wannan ƙarin ya samo asali ne daga tashin farashin danyen mai da ya kusa kai $120 a kowace ganga a makon jiya, kafin ya tsaya a kan $112 sakamakon yaƙin Amurka, Isra'ila da Iran.

Wannan ya sa matatar Dangote ma ta ƙara farashin dake fita daga matatar daga ₦1,175 zuwa ₦1,245 a kan kowace lita. Sakamakon haka, masu gidajen mai sun sauya farashinsu zuwa tsakanin ₦1,310 zuwa ₦1,400.

A birnin Legas, direbobin motocin kasuwa sun koka kan yadda ribarsu ke raguwa, inda gidajen mai na NNPCL ma suka ƙara farashi har sau biyu a cikin kwanaki kaɗan.

Toheeb Sulaimon, wani direban mota, ya ce samunsa na kullum ya ragu sosai; inda a baya yake kashe ₦9,000 wajen sayen mai, yanzu yana kashe sama da ₦20,000.

Farashin fetur a Arewacin Najeriya

Kara karanta wannan

An samu matsala: Dangote ya ƙara kuɗin fetur, lita ta haura N1240

A birnin Kano kuwa, farashin ya haura zuwa ₦1,390 a gidajen mai na masu zaman kansu kamar AA Rano. Wannan ya sa 'yan acaba da masu keke-napep ƙara kuɗin zirga zirgarsu.

Wani mazaunin garin Kano, Ismail Mabo, ya bayyana cewa an caje shi ₦4,000 kan tafiyar da a baya ake yin ta a kan ₦1,000.

Legit Hausa ta samu labari cewa wasu matafiya sun saye litar man fetur a kan N1, 300 a safiyar ranar Lahadi, sai dai da alama farashin yana ta kara tashi a yanzu.

A birnin Abuja ma, farashin ya tashi zuwa tsakanin ₦1,361 da ₦1,370 bayan sabon tsarin farashi da kamfanin MRS Oil ya fitar.

A jihar Kwara ma, musamman a Ilorin, ana sayen litar fetur tsakanin ₦1,295 zuwa ₦1,343. Wata ma'aikaciyar gwamnati, Oladuni Lateefat, ta bayyana cewa albashinsu ba ya iya biyan buƙatun sufuri da na gida a yanzu, kuma tana tunanin ajiye motarta.

Matatar man fetur a makon jiya ta kara kudin fetur yayin da ka samu karin kudin danyen mai a duniya.
Wani ma'aikaci na zuba fetur a babur din d'an acaba. Hoto: Light Oriye Tamunotonye / AFP via Getty Images
Source: Getty Images

Direbobin mota sun hakura da aiki

Wani mai mota, Mista Fidelis Nte, ya bayyana wa jaridar Nigerian Tribune a jiya Lahadi cewa ya daina fita aiki da motarsa yanzu.

Kara karanta wannan

Bukukuwan Sallah: Jerin gwamnonin Arewa 5 da za su biya albashin Maris da wuri

A cewarsa, daga babban yankin Legas (Mainland) zuwa Victoria Island, yanzu tana cinye masa ₦20,700 a kowace tafiya ɗaya, maimakon ₦12,900 da yake kashewa a farkon watan Fabrairu lokacin da lita take ₦860.

Shi ma wani mai motar, Ayo Adebisi, ya bayyana cewa ba zai iya ci gaba da sayen litar mai 10 a kowace rana ba, wanda yanzu farashin litar ya tashi zuwa tsakanin ₦1,360 da ₦1,380.

Yakin Iran: Dangote ya kara kuɗin fetur

Tun da fari, mun ruwaito cewa, matatar Dangote ta kara farashin man fetur da take sayarwa abokan huldarta da ₦70, wanda ke nufin lita daya yanzu ta koma ₦1245.

Sabon farashin zai fara aiki ne daga karfe 12:00 na daren yau Asabar, kuma zai shafi har da man da aka biya kudinsa amma ba a dauka ba.

An dora alhakin wannan karin kudin a kan tashin hankalin da ake fama da shi a Gabas ta Tsakiya wanda ya shafi farashin danyen mai.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com