Majalisar Wakilai Ta Amince Tinubu Ya Karbo Bashin Dala Biliyan 2.3 daga Ketare

Majalisar Wakilai Ta Amince Tinubu Ya Karbo Bashin Dala Biliyan 2.3 daga Ketare

  • Shugaba Bola Ahmed Tinubu zai kara ciyo bashi daga kasashen ketare domin cike gibin kasafin kudin 2025
  • Hakan dai ya biyo bayan amincewar da Majalisar Wakilai ta yi da batun karbo bashin Dala biliyan 2.3 daga kasashen ketare
  • Ta ce za a yi amfani da kudin wajen biyan bashin Eurobond, wanda wa'adinsa zai kare a watan Nuwamba, 2025 don kare mutuncin Najeriya

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja, Najeriya - Majalisar Wakilai ta kasa ta amince da bukatar Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu na karbo bashin Dala biliyan 2.3 daga kasashen waje.

Kara karanta wannan

Taraba: Rigima ta barke kan mallakar Masallacin Juma’a na Izalah, an rasa rai

Shugaba Bola Tinubu ya nemi izinin dauko wannan rance ne domin rage gibin kasafin kudin 2025 da kuma biyan wasu tsofaffin bashin Eurobond na Najeriya.

Majalisar Wakilai
Hoton zauren Majalisar Wakilan Tarayya da ke Abuja Hoto: HouseNGR
Source: Facebook

Premium Times ta tattaro cewa Majalisar ta amince da bukatar ciyo bashin ne bayan karbar rahoton kwamitin tallafi da harkokin bashi a zaman yau Laraba.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Shugaban Kwamitin Majalisa kan Tallafi, Rance da Gudanar da Bashi, Hon. Abubakar Nalaraba (APC, Nasarawa) ne ya gabatar da rahoton a zauren majalisar.

Rahoton ya nemi majalisa ta amince gwamnatin tarayya ta aiwatar da shirin nemo rance da kuma sake biyan tsofaffin bashin da aka tanada a cikin Kasafin Kudin 2025.

Shawarwarin da kwamitin ya ba Majalisa

Kwamitin ya shawarci Majalisar Wakilai da ta amince da karbo sabon bashi daga waje na Naira tiriliyan 1.84 (kimanin Dala biliyan 1.23) domin cike gibin kasafin kuidin shekarar 2025.

Haka kuma, ya bukaci majalisar da ta amince da biyan bashin Eurobond na Dala biliyan 1.12 (Wanda wa'adinsa ke karewa a watan Nuwamba 2025) domin gujewa rashin biyan bashi da kare mutuncin Najeriya a kasuwar bashi ta duniya.

Kara karanta wannan

Bayan karbar bukatar Tinubu, majalisa ta sa lokacin tantance sababbin hafsoshin tsaro

Bayan gabatar da rahoton, Majalisa ta tattauna kan lamarin tare da yanke hukuncin karshe kan bukatar shugaban kasa.

Yadda Majalisa ta amince da ciyo bashin

A yayin tattaunawa, Mataimakin Shugaban Masu Rinjaye, Hon. Abdullahi Halims (APC, Kogi), ya nemi kawo cikas, inda ya roki a jinkirta amincewa da rahoton domin a kara nazari kan shirin neman bashin.

Sai dai Shugaban Majalisar, Rt. Hon. Abbas Tajudeen, wanda ya jagoranci zaman, ya nuna rashin jin daɗinsa da wannan shawara, yana cewa:

“Ban ji daɗin wannan magana a kan batun da ba a kai ga cimma matsaya ba. Ina roƙonka da ka janye ta.”
Shugaban Majalisar Wakilai, Tajudeen Abbas.
Hoton Kakakin Majalisar Wakilai, Rt. Hon. Tajudeen Abbas a lokacin da yake jagorantar zama a Abuja Hoto: @SpeakerAbbas
Source: Twitter

Daga nan Hon. Abdullahi Halims ya janye kokensa, kuma majalisar ta ci gaba da amincewa da shawarwarin kwamitin daya bayan daya, kamar yadda Punch ta rahoto.

A ƙarshe, Majalisar ta amince da rahoton gaba ɗaya, kuma ta ba da cikakken izini ga gwamnatin tarayya ta karbo wannan bashin daga kasashen waje.

Majalisa na shirin gyara dokar EFCC

A baya, kun ji cewa majalisar wakilai ta fara karatu kan kudirin da ke neman gyara dokar kafa EFCC domin bai wa hukumar 'yancin cin gashin kanta.

Kara karanta wannan

Takaitaccen bayani game da sababbin hafsoshin tsaron da Tinubu ya nada

Dan majalisar wakilai daga jihar Filato, Yusuf Gagdi, ke ya jagoranci tattaunawa kan muhimman dalilan da kudirin ya kunsa.

Daya daga cikin muhimman abubuwan da kudirin ya kunsa shi ne rage ikon shugaban kasa wajen cire shugaban hukumar EFCC.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262