Wata Sabuwa: Lauyoyi Na Shirin Kawo Cikas ga Tabbatar da Nadin Shugaban INEC a Majalisa
- Bola Tinubu ya nada Farfesa Joash Amupitan a matsayin sabon shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC)
- Wata gamayyar kungiyar lauyoyi ta nuna rashin gamsuwarta kan nadin da Mai girma Shugaba Bola Tinubu ya yi
- Ta mika bukatarta gaban majalisar dattawa kan shirin tabbatar da Farfesa Amupitan a shugabancin hukumar INEC
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
FCT, Abuja - Wata gamayyar lauyoyi fiye da 1,000 da ke aiki karkashin kungiyar Association of Legislative Drafting and Advocacy Practitioners (ALDRAP) ta yi kira majalisar dattawa.
Kungiyar ALDRAP ta bukaci majalisar dattawa ta ki amincewa da nadin Farfesa Joash Ojo Amupitan, SAN, a matsayin sabon shugaban hukumar zaɓe mai zaman kanta ta kasa (INEC).

Source: Facebook
Jaridar Vanguard ta ce hakan na kunshe ne a cikin wata wasika da kungiyar ta rubuta a ranar 10 ga Oktoba, 2025.

Kara karanta wannan
Da gaske sabon shugaban INEC na cikin lauyoyin Tinubu a zaben 2023? an samu bayanai
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Lauyoyi sun koka kan nadin Joash Amupitan
An aika wasikar wadda sakataren kungiyar, Jesse Williams Amuga, ya sanyawa hannu ga shugaban kwamitin zaɓe na majalisar dattawa, Sanata Simon Lalong.
Kungiyar ta zargi Farfesa Amupitan da rashin cancanta saboda rawar da ya taka a baya a matsayin lauyan jam’iyyar APC yayin da ake sauraron karar zaɓen shugaban kasa na 2023 a Kotun Koli.
Ta ce bai kamata majalisar dattawa ta tabbatar da nadin Farfesa Amupitan ba, sai dai ta sanar da shugaban kasa cewa bai cika ka’idodin da kundin tsarin mulki ya tanada ba.
“Majalisar Dattawa ta riga ta kafa misali tun a 2021 lokacin da ta ki amincewa da nadin Lauretta Onochie saboda alakarta da jam’iyyar APC. Hakan ya zama ka’ida, kuma lamarin Farfesa Amupitan ya yi kama da irin na ta."
- Jesse Williams Amuga
Wace bukata aka nema a majalisar dattawa?
“Tun da ya riga ya yi aiki a matsayin babban lauya ga jam’iyyar APC, Farfesa Amupitan ba zai iya gudanar da aikinsa a matsayin shugaban INEC cikin gaskiya ba, musamman a zaɓen da ya shafi APC da sauran jam’iyyu."
- Jesse Williams Amuga
ALDRAP ta jaddada cewa Najeriya na da lauyoyi sama da 200,000 wadanda fiye da rabinsu ba su da alaka da kowace jam’iyyar siyasa, kuma za a iya zaɓar ɗaya daga cikinsu ba tare da an nuna son kai ba.

Source: Twitter
Ƙungiyar ta gargadi majalisar dattawa cewa idan ta tabbatar da nadin Amupitan, za ta daukaka kara a kotu.
"Idan majalisar dattawa ta tabbatar da Farfesa Joash Amupitan, kungiyarmu ba za ta yi wasa ba wajen kai kara domin tilasta bin ka’idar rashin nuna bambanci wajen tabbatar da shugaban INEC."
- Jesse Williams Amuga
Sai dai bincike ya nuna cewa Farfesa Joash Amupitan bai da alaka da APC kuma bai cikin lauyoyin Bola Tinubu a shari'ar zaben 2023.
ADC ta aika da sako ga Amupitan
A wani labarin kuma, kun ji cewa jam'iyyar ADC mai adawa a Najeriya ta yi kira ga sabon shugaban hukumar INEC na kasa, Farfesa Joash Amupitan.
ADC ta bukaci sabon shugaban na INEC da ya zama mai amana ga 'yan Najeriya wajen sauke nauyin da aka dora masa.
Ta bukaci ka da ya yarda ya zama dan amshin shatan gwamnati yayin jagorancin da zai yi a hukumar INEC.
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng

