Ana Murnar Fara Azumi, Sanatan Arewa Ya Shirya Gagarumin Bikin Tallafawa Talakawa

Ana Murnar Fara Azumi, Sanatan Arewa Ya Shirya Gagarumin Bikin Tallafawa Talakawa

  • Sanata Saliu Mustapha ya horar da mutane fiye da 2,500 a Kwara kan harkar noma, kasuwanci da sana’o’i, tare da raba masu kayan aiki
  • Mataimakin shugaban majalisar dattawa, Barau Jibrin, da ministan noma, Abubakar Kyari, sun halarci taron domin karfafa Sanata Saliu
  • An gudanar da taron a Ilorin, inda Sanata Jibrin da takwarorinsa suka bayar da injunan dinki 200 don tallafawa al’ummar Kwara ta Tsakiya

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Kwara - Sanata Saliu Mustapha ya bai wa mutane fiye da 2,500 tallafi domin bunkasa harkokin kasuwanci, noma, da sana’o’in hannu a jihar Kwara.

Wannan tallafin na zuwa ne yayin da al'ummar Musulmi a Najeriya da kasashen duniya ke murnar fara azumin watan Ramadan na 2025.

Sanata Saliu Mustapha ya yi magana da ya rabawa mutane 2,500 tallafi
Sanatan Kwara ta Tsakiya ya rabawa sama da mutane 2500 tallafi na kayayyaki daban daban. Hoto: @RealMallamSaliu
Asali: Twitter

Mataimakin shugaban majalisar dattawa, Barau Jibrin, da ministannoma, Abubakar Kyari, sun yabawa Sanata Saliu da kawo wannan shiri, inji rahoton Punch.

Kara karanta wannan

Mataimakin shugaban Majalisa ya goyi bayan kudirin ƙirkiro jiha 1 a Arewa, an faɗi sunanta

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sanatan Kwara ya tallafawa 'yan mazabarsa

Sanata Barau da Abubakar Kyari sun ce wannan shirin na Sanata Saliu ya yi daidaita da manufofin Shugaba Bola Tinubu na inganta rayuwar al'umma.

Sanata Saliu, mai wakiltar Kwara ta Tsakiya (APC), ya raba kayan tallafi ga mata, manoma, da masu sana’o’i a birnin Ilorin na jihar Kwara.

Ya ce shirin zai taimaka wajen tabbatar da cewa masu cin gajiyar shirin sun dogaro da kansu ta hanyar basu kayan aiki da horo na musamman.

"Shirin da aka gabatar na yau ya nuna manufarmu ta tallafawa dukkanin wadanda muka horar da su. Mun yanke shawarar horar da su a matakai daban daban.
“Mun horar da su kan yadda ake hadawa, gyarawa da kula da na'urorin ba da wuta da hasken rana, kuma za su sami kayayyakin aiki yau."

- Inji Sanata Mustapha.

Barau ya yi magana a taron ba da tallafin

Kara karanta wannan

Ramadan: Ɗan majalisa a Arewa ya tara talakawa, ya raba masu kudi da kayan abinci

An gudanar da shirin mai taken: 'Alubarika 1.0: Shirin bunkasa mutane kan noma da gina rayuwa' a birnin Ilorin, a ranar Juma’a.

Sanata Barau Jibrin ya yi magana da ya je taya Sanata Saliu Mustapha raba kayan tallafi a Kwara
Sanata Barau Jibrin da wasu sanatoci sun tallafawa 'yan Kwara ta tsakiya da injina. Hoto: @RealMallamSaliu
Asali: Twitter

Sanata Jibrin da sauran ‘yan majalisa sun bayar da gudunmawar injunan dinki 200 ga al’ummar Kwara ta Tsakiya..

Mataimakin shugaban majalisar ya ce:

“Mun hallara a nan a yau domin karfafawa Sanata Mustapha saboda kokarinsa wajen bunkasa noma da ci gaban al'ummar mazabarsa.”

Sanata Jibrin ya jaddada cewa noma na da matukar muhimmanci, domin babu wata al’umma da za ta cigaba ba tare da abinci ba.

Ya kara da cewa shirin da Sanata Saliu ya gudanar ya dace da kudirin Shugaba Tinubu na samar da abinci ga kowa a Najeriya.

Ministan noma ya jinjinawa kokarin Sanata Saliu

Ministan noma, Abubakar Kyari, ya yabawa Sanata Mustapha bisa jajircewarsa wajen aiwatar da ayyukan da ke inganta samar da abinci a kasa.

Kara karanta wannan

Yaki da zaman kashe wando: Sanata Goje ya raba miliyoyi da kayayyaki

Kyari ya ce irin wadannan shirye-shirye na tallafawa gwamnati wajen tabbatar da wadatar abinci da rage fatara a Najeriya.

Masu cin gajiyar shirin sun nuna godiyarsu, suna masu cewa hakan zai bunkasa harkokinsu na kasuwanci, noma da kuma rayuwarsu ta yau da kullum.

Duba hotunan taron da sanatan ya dora a shafinsa na X.

Dan majalisa ya rabawa talakawa 5000 tallafi

A wani labarin, mun ruwaito cewa, dan majalisar Kaga/Magumeri/Gubio a jihar Borno, Hon. Usman Zannah, ya tallafawa al’ummarsa yayin da aka fara azumin Ramadan.

Kayayyakin tallafin da dan majalisar ya raba sun haɗa da shinkafa, sukari, taliya da kudi, wanda ya ce ya saba rabawa domin al'umma su yi azumi cikin walwala.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.