'Can Ta Matse Musu': Ribadu Ya Fusata da Aka Wulakanta Hafsan Tsaron Najeriya a Ketare

'Can Ta Matse Musu': Ribadu Ya Fusata da Aka Wulakanta Hafsan Tsaron Najeriya a Ketare

  • Mai ba shugaban ƙasa shawara kan tsaro, Nuhu Ribadu, ya soki gwamnatin Canada dakile hafsan tsaro, Christopher Musa shiga kasar
  • An gayyaci Janar Musa da tawagarsa zuwa taron girmamawa ga tsofaffin sojoji a Canada, amma wasu ba su samu damar shiga ba
  • Ribadu ya kira matakin da rashin girmamawa, yayin da hafsun ya yi kira ga Najeriya ta tsaya da kafafunta a fagen siyasa na duniya

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Mai ba shugaban ƙasa shawara kan tsaro, Nuhu Ribadu, ya soki gwamnatin Canada saboda hana 'visa' ga Hafsan Tsaron Najeriya, Christopher Musa.

Nuhu Ribadu ya nuna bacin ransa kan matakin gwamnatin kasar inda suka hana Janar Musa da wasu manyan jami’an soja shiga cikinta.

Ribadu ya soki Canada kan wulakanta hafsan tsaron Najeriya
Nuhu Ribadu ya nuna rashin jin dadi kan kin barin Hafsan tsaron Najeriya shiga cikinta. Hoto: HQ Nigerian Army, Nuhu Ribadu.
Asali: Facebook

Yadda Canada ta wulakanta hafsan tsaron Najeriya

Kara karanta wannan

An kaddamar da shirin karban tuban 'yan bindiga da koya musu sana'o'i

Jami’an sun shirya halartar wani taro a Kanada na girmama tsofaffin sojoji, amma ba duka suka samu bisa ba, cewar Vanguard.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Lamarin ya haifar da martani mai zafi daga hukumomin Najeriya inda suke ganin hakan rashin girmama wa ne.

Nuhu Ribadu da Musa sun yi jawabi ne a wani taro na farko na shekara-shekara na kungiyar daliban tsofaffin makarantar tsaro ta kasa (AANISS) a Abuja.

Ribadu ya fusata da matakin gwamnatin Canada

Ribadu ya sake jaddada muhimmancin yin kokarin bunkasa Najeriya, yana mai cewa wannan al’amari ya kara masa kwarin gwiwa wajen kawo cigaba.

Har ila yau, Ribadu yaba wa Musa kan jagorancin da yake bayarwa wajen yaki da matsalar tsaro, tare da kira ga hadin gwiwa tsakanin hukumomin tsaro.

"Na yaba da yadda ka fito fili ka fadi cewa Canada ta hana ka bisa, can ta matse musu, koda yake abin yana da zafi kuma rashin girmamawa ne, mu mutane masu zaman lafiya ne kuma masu karfi, ya kamata mu gyara kasarmu."

Kara karanta wannan

Yadda gwamnatin tarayya ta nemi ba ni rashawar N5bn," Ɗan takarar shugaban ƙasa

- Nuhu Ribadu

Janar Musa ya fadi yadda lamarin ya afku

A bangarensa, Janar Musa ya jaddada bukatar Najeriya ta tsaya da kafafunta a duniya.

Janar Musa ya ce an gayyace shi da tawagarsa zuwa taron girmamawa amma aka hana wasu shiga, yana mai cewa lamarin abin takaici ne, cewar TheCable.

“An gayyace mu tare da tawagarmu, rabinmu sun je, amma an hana rabin shiga wanda hakan abin takaici ne.
“Wannan darasi ne ga Najeriya ta tsaya da kafafunta, ta tsaya da karfi a matsayin kasa, kuma kada a sake raina ta.”

- Janar Christopher Musa

Ribadu ya gargadi Naja'atu kan bidiyon TikTok

Mun ba ku labarin cewa Mai ba shugaban kasa shawara kan tsaro, Nuhu Ribadu, ya gargadi Naja’atu Muhammad ta janye kalamanta game da zarginsa a bidiyon TikTok.

Naja’atu ta zargi Ribadu da goyon bayan Bola Tinubu, wanda a baya ya soka a lokacin da yake shugaban EFCC da cewa yana dagacikin mafi rashin gaskiya a 'yan siyasa.

Kara karanta wannan

"An ba Tinubu gurguwar shawara," Ɗan Majalisa ya tona kura kuran da aka gano a ƙudirin haraji

Daga bisani, Naja'atu ta yi martani inda ya ce ba za ta janye kalamanta ba kuma a shirye take ta kare kanta saboda tana da hujjoji.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.