Sojoji Sun Samu Nasara a Kaduna, Tantiran Masu Safarar Makamai Sun Shiga Hannu

Sojoji Sun Samu Nasara a Kaduna, Tantiran Masu Safarar Makamai Sun Shiga Hannu

  • Dakarun sojojin Najeriya sun samu nasarar cafke wasu mutane da ake zargin masu safarar makamai ne a jihar Kaduna da ke yankin Arewa maso Yamma
  • Sojojin na rundunar Operation Safe Haven sun cafke mutanen ne guda biyu a ƙauyen Fadiya da ke ƙaramar hukumar Zangon Kataf ta jihar Kaduna
  • Bayan cafke mutanen da ake zargin, dakarun sojojin sun kuma ƙwato makamai masu yawa da suka haɗa da bindigogi da alburusai

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Kaduna - Dakarun sojojin sashe na bakwai na rundunar Operation Safe Haven sun kama wani shahararren mai safarar makamai tare da abokin aikinsa, a jihar Kaduna.

Dakarun sojojin sun ƙwace tarin makamai da alburusai yayin samamen wanda suka gudanar a jihar Kaduna.

Sojoji sun cafke masu safarar makamai a Kaduna
Masu safarar makamai sun shiga hannun sojoji a Kaduna Hoto: Legit.ng
Asali: Twitter

Masani kan harkokin tsaro a yankin Arewa maso Gabas da Arewacin Najeriya, Zagazola Makama, ya bayyana hakan a shafinsa na X.

Kara karanta wannan

Jami'an DSS sun cafke mai safarar makamai daga Nijar zuwa Najeriya

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Yadda sojoji suka cafke masu safarar makamai

Dakarun sojojin sun gudanar da samamen ne a ranar Lahadi, 20 ga watan Janairu, bayan samun bayanan sirri kan ayyukan masu laifin.

Wata majiya ta bayyana cewa an cafke waɗanda ake zargin ne a ƙauyen Fadiya da ke ƙaramar hukumar Zangon Kataf.

Majiyar ta bayyana sunayen waɗanda ake zargin a matsayin Timothy Yusuf mai shekaru 62 da ɗansa Timothy Obadiah.

A cewar majiyar, waɗanda ake zargin sun dade suna gudanar da ayyukan safarar makamai a yankin, lamarin da ya zama barazana ga tsaro

Sojoji sun ƙwato mugayen makamai

A lokacin samamen, sojojin sun ƙwace bindigogi 11, jigida ta bindigar AK-47 guda biyu da kuma harsasan NATO guda 60 masu kaurin 7.62mm.

“Masu laifin da makaman da aka ƙwace suna tsare don gudanar da bincike, yayin da ake ci gaba da ƙoƙarin gano sauran mambobin ƙungiyar masu safarar makaman."

- Wata majiya

Wannan nasarar dai, na daga cikin ƙoƙarin gwamnati da jami'an tsaro wajen kawo ƙarshen matsalar rashin tsaro a yankin.

Kara karanta wannan

An kama motar makamai ana shirin shigo da ita Najeriya daga kasar Nijar

Jami'an tsaro a Najeriya na ci gaba da ƙara zage damtse wajen kawo ƙarshen miyagu waɗanda ke barazana ga zaman lafiyar ƙasar nan.

Karanta wasu labaran kan dakarun sojoji

Sojoji sun ragargaji ƴan bindiga

A wani labarin kuma, kun ji cewa dakarun sojojin Najeriya na rundunar Operation Fansan Yamma sun yi dirar mikiya kan sansanonin ƴan bindiga a jihohin Keebi da Sokoto.

Sojojin waɗanda suka gudanar da samamen a wasu ƙananan hukumomin jihohin biyu, sun samu nasarar hallaka ƴan bindiga masu yawa tare da lalata sansanoninsu.

Kara karanta wannan

Rundunar sojoji ta sake taso Bello Turji a gaba, ta fadi abin kunyar da ya yi

Farmakin da gwarazan dakarun sojojin suka kai kan ƴan bindigan ya tilastawa da yawa daga cikinsu tserewa daga maɓoyarsu domin tsira da rayukansu.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng