Gwamnan Kano Ya Ware N4.8bn Domin Gyara Makarantu, Mutane 17, 000 Za Su Samu Aiki
- Gwamnatin jihar Kano karkashin gwamna Abba Kabir Yusuf ta ware makudan kudi domin yin ayyuka na musamman a ɓangare ilimi
- Rahotanni sun nuna cewa ayyukan za su shafi dukkan kananan hukumomin jihar guda 44 domin inganta ilimin karkara da birni
- Daraktan yada labaran gwamnatin jihar, Sanusi Bature Dawakin-Tofa ya yi karin haske kan ayyukan da ma'aikata da za a dauka a jihar
Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.
Jihar Kano - Gwamnan Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf ya ware makudan kudi domin haɓaka ilimi a dukkan fadin jihar.
Gwamnatin jihar ta tabbatar da cewa manyan ayyukan za su shafi dukkan sassan jihar ciki har da ƙauyuka.

Asali: Facebook
Legit ta gano haka ne cikin wani sako da daraktan yada labaran gwamnatin Kano, Sanusi Bature Dawakin-Tofa ya wallafa a shafinsa na Facebook.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Kano: Za a gyara makarantun firamare
Sanusi Bature Dawakin-Tofa ya tabbatar da cewa gwamnatin ta ware N1.9b domin gyare-gyaren makarantun firamare a jihar.
Ya kuma kara da cewa kwaskwarimar za ta shafi dukkan makarantun firamare da suke kananan hukumomin jihar guda 44.
Za a gina sababbin ajujuwa a Kano
Har ila yau, Abba Kabir Yusuf ya ware kudi kimanin N2.9b domin gina ajujuwa a fadin jihar, rahoton Daily Trust.
Rahotanni sun nuna cewa gwamnan ya ce za a yi amfani da kuɗin ne domin gina ajujuwa a makarantun firamare saboda inganta ilimi daga tushe.
Za a dauki ma'aikata a makarantun Kano
Har ila yau, gwamantin ta tabbatar da cewa za a ɗauki masu gadi 17,600 a makarantun jihar domin inganta tsaro.

Kara karanta wannan
Gwamnatin Kano ta ware miliyoyi kan kiwon lafiya, ta yi albishir ga masu cutar sikila
An bayyana cewa kowace karamar hukuma a jihar Kano za ta samu masu gadi 400 domin kare makarantun jihar.
Gwamnatin Kano ta soke lasisin makarantu
A wani rahoton, kun ji cewa gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano ya soke lasisin makarantu masu zaman kansu gaba daya a jihar kwanaki.
Wannan na daga cikin matakin da gwamnati ke yi na tabbatar da makarantun sun cike tsari da ka'idoji domin samun ilimi mai inganci.
Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.
Asali: Legit.ng