Fadar Shugaban Kasa ta Fadi Ranar da Shugaba Tinubu zai Yiwa 'yan Najeriya Jawabi
- Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu zai yi jawabi ga 'yan Najeriya yayin da ake bikin dimukuradiyya ranar Laraba
- Mashawarcin shugaban kasa kan kafafen yada labarai, Cif Ajuri Ngalale ne ya sanar da haka a yau, inda ya ce shugaban zai yi jawabi ta manyan kafafen yada labarai
- A gobe Laraba ne za a yi bikin ranar dimukuradiyya da tsohon shugaba Muhammadu Buhari ya sauya zuwa 12 ga watan Yuni domin martaba MKO Abiola
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.
Abuja- Yayin da ake shirin bikin ranar dimukuradiyya a gobe Laraba, fadar shugaban kasa ta bayyana cewa shugaba Bola Ahmed Tinubu zai yiwa 'yan kasa jawabi.
![](https://cdn.legit.ng/images/360x203/f5bcf68b2bbd1596.jpeg?v=1)
Kara karanta wannan
"Abin da ya sa Bola Tinubu ya fi Atiku da Obi cancantar zama shugaban ƙasa a 2023"
Mashawarcin shugaban kasa na musamman kan yada labarai, Cif Ajuri Ngelale ne ya sanar da hakan a sanarwar da ya fitar yau Talata.
![Bola Tinubu Bola Tinubu](https://cdn.legit.ng/images/1120/d625b57e6b2b81ea.jpeg?v=1)
Asali: Facebook
Mista Ngelale ta sakon da ya wallafa a shafinsa na facebook ya bayyana cewa shugaba Bola Tinubu zai yi jawabin da za a watsa a kafafen yada labarai.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Tinubu zai yi bayani da safe
Da misalin 7:00 na safiyar gobe Laraba ne ake sa ran shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu zai yi jawabi ga 'yan Najeriya a wani bangare na bikin ranar dimukuradiyya kamar yadda Nigerian Tribune ta wallafa.
Mashawarcin shugaba Tinubu kan kafafen yada labarai, Ajuri Ngalale ya ce za a yada jawabin shugaban kasar a tashar talabijin ta NTA da radiyon tarayya ta FRCN.
Tun a shekarar 2018 tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ya sauya ranar dimukuradiyyar kasar nan daga 29 ga watan Mayu zuwa 12 Yuni domin martaba MKO Abiola.
![](https://cdn.legit.ng/images/360x203/0281d6dcbded45dc.jpeg?v=1)
Kara karanta wannan
NLC na neman ƙarin albashi, Tinubu ya bayyana wani muhimmin aiki da zai yi zuwa 2030
Ranar dimukuradiyya: An bayar da hutu
A wani labarin kun ji cewa gwamnatin tarayya ta ba 'yan Najeriya hutun kwana daya a wani bangare na bikin ranar dimukuradiyya a gobe Laraba.
Ministan harkokin cikin gida, Olubunmi Tunji-Ojo ne ya bayyana haka a sanarwar da ya fitar, inda ya bukaci 'yan Najeriya su rika yaba kokarin da shugaba Tinubu ke yi.
Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.
Asali: Legit.ng