Gwamnatin Kano Ta Yi Magana a Kan Rahoton Bullar Rashin Tsaro a Jihar

Gwamnatin Kano Ta Yi Magana a Kan Rahoton Bullar Rashin Tsaro a Jihar

  • Gwamnatin Kano ta bayyana rahoton cewa akwai rashin tsaro a jihar a matsayin labaran karya da bai dace a rika yadawa ba ganin yadda ake zaman lafiya
  • Mataimakin Gwamnan jihar, Kwamred Aminu AbdulSalam Gwarzo ne ya musanta labarin a ranar Litinin, inda ya ce akwai rashin adalci a yada babu tsaro a Kano
  • Ya ce Kano na daga jihohi mafi ingantaccen tsaro a tarayyar Najeriya, da ma yankin Afrika ta yamma, saboda haka kowa ya shigo ya yi kasuwanci ba tare da tsoro ba

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

Jihar Kano-Gwamnatin Kano ta ta musanta labarin cewa akwai matsalar rashin tsaro a jihar kamar yadda wasu rahotanni ke bayyanawa.

Kara karanta wannan

Operation kauda badala: Hisbah ta damke maza da mata 20 suna wanka tare a Kano

Mataimakin Gwamnan Kano, Aminu AbdulSalam Gwarzo ne ya musanta zargin a ranar Litinin, inda ya ce rashin adalci ne a ce babu zaman lafiya a Kano.

Comrade Aminu AbdulSalam Gwarzo
Gwamnatin ta ce babu maganar rashin tsaro a Kano Hoto: @Aminugwarzo
Asali: Twitter

Akwai matsalar tsaro a jihar Kano?

Kwamered Aminu AbdulSalam Gwarzo ya bayyana haka ne yayin bikin bude makon shari’a a shekarar 2024, kamar yadda Leadersip News ta wallafa.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A kalamansa:

“Kano na daga wurare mafi tsaro a Najeriya, ko ma Afrika ta yamma.”

“Akwai tsaro a Kano,” Kwamred AbdulSalam

Gwamnatin jihar Kano ta bayyana cewa kano wuri ne da kowa ya kamata ya shigo ba tare da jin dar-dar a zuciyarsa ba.

Mataimakin gwamna, Kwamred Aminu AbdulSalam Gwarzo ne ya bayyana haka a ranar Litinin, inda ya ce Kano wuri ne da ya kamata a shigo domin yin kasuwanci, kuma yayata labarin babu tsaro a jihar rashin adalci ne.

Kara karanta wannan

"Daurarru 400 a Kano ba su san makomarsu a gidan yari ba," Inji 'Yan Sanda

Ko a baya rundunar 'yan sandan Kano ta bayyana cewa ta na sintiri a iyakokin jihar domin tabbatar da tsaro, da hana bata-gari tsallakowa jihar, kamar yadda Punch News ta wallafa.

Mataimakin gwamnan ya ce labarin rashin tsaro a Kano labaran karya ne kawai, kuma bai dace a dinga yayata wannan labarin marar dadin ji ba.

An kama ‘yan daba 61 a Kano

A baya mun ba ku labarin cewa rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta kama wasu ‘yan daba kimanin 61 da su ka addabi jihar.

An kama ‘yan daban ne a sassan masarautun jihar guda biyar a daidai lokacin da ake ci gaba da bukukuwan sallah karama a fadin Kano.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano.